< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
At this also my heart trembleth, and is moved out of its place.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Hearken ye unto the noise of his voice, and the sound that goeth out of his mouth.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
He sendeth it forth under the whole heaven, and his lightning unto the ends of the earth.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
After it a voice roareth; he thundereth with the voice of his majesty: and he stayeth them not when his voice is heard.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
God thundereth marvelously with his voice; great things doeth he, which we cannot comprehend.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
For he saith to the snow, Fall thou on the earth; likewise to the shower of rain, and to the showers of his mighty rain.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
He sealeth up the hand of every man; that all men whom he hath made may know [it].
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Then the beasts go into coverts, and remain in their dens.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Out of the chamber [of the south] cometh the storm: and cold out of the north.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
By the breath of God ice is given: and the breadth of the waters is straitened.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Yea, he ladeth the thick cloud with moisture; he spreadeth abroad the cloud of his lightning:
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
And it is turned round about by his guidance, that they may do whatsoever he commandeth them upon the face of the habitable world.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Whether it be for correction, or for his land, or for mercy, that he cause it to come.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Hearken unto this, O Job: stand still, and consider the wondrous works of God.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Dost thou know how God layeth [his charge] upon them, and causeth the lightning of his cloud to shine?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Dost thou know the balancings of the clouds, the wondrous works of him which is perfect in knowledge?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
How thy garments are warm, when the earth is still by reason of the south [wind]?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Canst thou with him spread out the sky, which is strong as a molten mirror?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Teach us what we shall say unto him; [for] we cannot order [our speech] by reason of darkness.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Shall it be told him that I would speak? or should a man wish that he were swallowed up?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
And now men see not the light which is bright in the skies: but the wind passeth, and cleanseth them.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Out of the north cometh golden splendour: God hath upon him terrible majesty.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
[Touching] the Almighty, we can not find him out; he is excellent in power: and in judgment and plenteous justice he will not afflict.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Men do therefore fear him: he regardeth not any that are wise of heart.

< Ayuba 37 >