< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
Ja, derover skælver mit Hjerte, bævende skifter det Sted!
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Lyt dog til hans bragende Røst, til Drønet, der gaar fra hans Mund!
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Han slipper det løs under hele Himlen, sit Lys til Jordens Ender;
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
efter det brøler hans Røst, med Højhed brager hans Torden; han sparer ikke paa Lyn, imedens hans Stemme høres.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Underfuldt lyder Guds Tordenrøst, han øver Vælde, vi fatter det ej.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Thi han siger til Sneen: »Fald ned paa Jorden!« til Byger og Regnskyl: »Bliv stærke!«
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
For alle Mennesker sætter han Segl, at de dødelige alle maa kende hans Gerning.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
De vilde Dyr søger Ly og holder sig i deres Huler:
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Fra Kammeret kommer der Storm, fra Nordens Stjerner Kulde.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
Ved Guds Aande bliver der Is, Vandfladen lægges i Fængsel.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Saa fylder han Skyen med Væde, Skylaget spreder hans Lys;
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
det farer hid og did og bugter sig efter hans Tanke og udfører alt, hvad han byder, paa hele den vide Jord,
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
hvad enten han slynger det ud som Svøbe, eller han sender det for at velsigne.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Job du maa lytte hertil, træd frem og mærk dig Guds Underværker!
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Fatter du, hvorledes Gud kan magte dem og lade Lys straale frem fra sin Sky?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Fatter du Skyernes Svæven, den Alvises Underværker?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Du, hvis Klæder ophedes, naar Jorden døser ved Søndenvind?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Hvælver du Himlen sammen med ham, fast som det støbte Spejl?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Lær mig, hvad vi skal sige ham! Intet kan vi faa frem for Mørke.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Meldes det ham, at jeg taler? Siger en Mand, at han er fra Samling?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Og nu: Man ser ej Lyset, skygget af mørke Skyer, men et Vejr farer hen og renser Himlen,
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
fra Norden kommer en Lysning. Over Gud er der frygtelig Højhed,
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
og den Almægtige finder vi ikke. Almægtig og rig paa Retfærd bøjer han ikke Retten;
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
derfor frygter Mennesker ham, men af selv kloge ænser han ingen.

< Ayuba 37 >