< Ayuba 36 >
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Espérame un poco, y te enseñaré; porque todavía hablo por Dios.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Tomaré mi sabiduría de lejos, y daré la justicia a mi hacedor.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Porque de cierto no son mentira mis palabras; antes se trata contigo con perfecta sabiduría.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
He aquí que Dios es grande, y no aborrece; fuerte es en virtud de corazón.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
No dará vida al impío, antes a los humildes dará su derecho.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
No quitará sus ojos del justo; antes bien con los reyes los pondrá en silla para siempre, y serán ensalzados.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Y si estuvieren presos en grillos, y cautivos en las cuerdas de la bajeza,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
él les anunciará la obra de ellos, y que sus rebeliones prevalecieron.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Y despierta el oído de ellos para castigo, y les dice que se conviertan de la iniquidad.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Si oyeren, y le sirvieren, acabarán sus días en bien, y sus años en deleites.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mas si no oyeren, serán pasados a cuchillo, y perecerán sin sabiduría.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Pero los hipócritas de corazón lo irritarán más, y no clamarán cuando él los atare.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Fallecerá el alma de ellos en su juventud, y su vida entre los fornicarios.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Al pobre librará de su pobreza, y en la aflicción despertará su oído.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Asimismo te apartaría de la boca de la angustia a lugar espacioso, libre de todo apuro; y te asentará mesa llena de grosura.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Mas tú has llenado el juicio del impío, contra la justicia y el juicio que lo sustentan todo.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Por lo cual de temer es que no te quite con golpe, el cual no puedas apartar de ti con gran rescate.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
¿Por ventura estimará él tus riquezas, ni del oro, ni de todas las fuerzas de la potencia?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
No anheles la noche, en la cual él corta los pueblos de su lugar.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Guárdate, no mires a la iniquidad; teniéndola por mejor que la pobreza.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
He aquí que Dios es excelso con su potencia; ¿qué enseñador semejante a él?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
¿Quién le ha prescrito su camino? ¿Y quién le dirá: Iniquidad has hecho?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Acuérdate de engrandecer su obra, la cual contemplan los hombres.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
La cual vieron todos los hombres; y el hombre la ve de lejos.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
He aquí, Dios es grande, y nosotros no le conocemos; ni se puede rastrear el número de sus años.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Porque él detiene las goteras de las aguas, cuando la lluvia se derrama de su vapor;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
cuando gotean de las nubes, gotean sobre los hombres en abundancia.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
¿Si entenderá también los extendimientos de las nubes, y los bramidos de su tienda?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
He aquí que sobre él sobre extiende su luz, y cubrió las raíces del mar.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Con ellas castiga a los pueblos, y da comida a la multitud.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Con las nubes encubre la luz, y les manda que vayan contra ella.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
La una da nuevas de la otra; la una adquiere ira contra la que viene.