< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Y AÑADIÓ Eliú, y dijo:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Espérame un poco, y enseñarte he; porque todavía [tengo] razones en orden á Dios.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Tomaré mi noticia de lejos, y atribuiré justicia á mi Hacedor.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Porque de cierto no son mentira mis palabras; contigo [está] el que es íntegro en [sus] conceptos.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
He aquí que Dios es grande, mas no desestima á nadie: es poderoso en fuerza de sabiduría.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
No otorgará vida al impío, y á los afligidos dará su derecho.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
No quitará sus ojos del justo; antes bien con los reyes los pondrá en solio para siempre, y serán ensalzados.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Y si estuvieren prendidos en grillos, y aprisionados en las cuerdas de aflicción,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
El les dará á conocer la obra de ellos, y que prevalecieron sus rebeliones.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Despierta además el oído de ellos para la corrección, y díce[les] que se conviertan de la iniquidad.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Si oyeren, y [le] sirvieren, acabarán sus días en bien, y sus años en deleites.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mas si no oyeren, serán pasados á cuchillo, y perecerán sin sabiduría.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Empero los hipócritas de corazón lo irritarán más, y no clamarán cuando él los atare.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Fallecerá el alma de ellos en su mocedad, y su vida entre los sodomitas.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Al pobre librará de su pobreza, y en la aflicción despertará su oído.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Asimismo te apartaría de la boca de la angustia á lugar espacioso, [libre] de todo apuro; y te asentará mesa llena de grosura.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Mas tú has llenado el juicio del impío, [en vez] de sustentar el juicio y la justicia.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Por lo cual [teme] que [en su] ira no te quite con golpe, el cual no puedas apartar de ti con gran rescate.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
¿Hará él estima de tus riquezas, ni del oro, ni de todas las fuerzas del poder?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
No anheles la noche, en que desaparecen los pueblos de su lugar.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Guárdate, no tornes á la iniquidad; pues ésta escogiste más bien que la aflicción.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
He aquí que Dios es excelso con su potencia: ¿qué enseñador semejante á él?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
¿Quién le ha prescrito su camino? ¿y quién [le] dirá: Iniquidad has hecho?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Acuérdate de engrandecer su obra, la cual contemplan los hombres.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Los hombres todos la ven; mírala el hombre de lejos.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
He aquí, Dios es grande, y nosotros no le conocemos; ni se puede rastrear el número de sus años.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
El reduce las gotas de las aguas, al derramarse la lluvia según el vapor;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Las cuales destilan las nubes, goteando en abundancia sobre los hombres.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
¿Quién podrá tampoco comprender la extensión de las nubes, y el sonido estrepitoso de su pabellón?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
He aquí que sobre él extiende su luz, y cobija [con ella] las raíces de la mar.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Bien que por esos medios castiga á los pueblos, á la multitud da comida.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Con las nubes encubre la luz, y mándale [no brillar], interponiendo [aquéllas].
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Tocante á ella anunciará [el trueno], su compañero, [que hay] acumulación de ira sobre el que se eleva.

< Ayuba 36 >