< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Y pasando a delante Eliú, dijo:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Espérame un poco, y enseñarte he: porque todavía hablo por Dios.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Tomaré mi sabiduría de lejos, y daré la justicia a mi Hacedor.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Porque de cierto no son mentira mis palabras, antes se trata contigo con perfecta sabiduría.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
He aquí, que Dios es grande, y no aborrece, fuerte en virtud de corazón.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
No dará vida al impío; y a los afligidos dará su derecho.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
No quitará sus ojos del justo: mas con los reyes los pondrá también en trono para siempre, y serán ensalzados.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Y si estuvieren presos en grillos, y cautivos en las cuerdas de aflicción,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
El les anunciará la obra de ellos, y que sus rebeliones prevalecieron.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Y despierta el oído de ellos para castigo, y dice que se conviertan de la iniquidad.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Si oyeren, y sirvieren, acabarán sus días en bien, y sus años en deleites.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mas si no oyeren, serán pasados a cuchillo: y perecerán sin sabiduría.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Mas los hipócritas de corazón le irritarán más; y no clamarán, cuando él los atare.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
El alma de ellos morirá en su mocedad, y su vida entre los sodomíticos.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Al pobre librará de su pobreza, y en la aflicción despertará su oreja.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Y aun te apartará de la boca de la angustia en anchura, debajo de la cual no haya estrechura, y te asentará mesa llena de grosura.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Mas tú has henchido el juicio del impío contra la justicia, y el juicio [que lo] sustenta todo.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Por lo cual es de temer, que no te quite con herida, la cual no evites con gran rescate.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
¿Estimará él tus riquezas, ni el oro, ni todas las fuerzas de poder?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
No desees la noche, en la cual él corta los pueblos de su lugar.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Guárdate, no mires a la iniquidad, teniéndola por mejor que la pobreza.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
He aquí, que Dios será ensalzado con su poder, ¿quién semejante a él, enseñador?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
¿Quién visitó sobre él su camino? ¿Y quién dijo: Iniquidad has hecho?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Acuérdate de engrandecer su obra, la cual contemplan los hombres.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
La cual vieron todos los hombres, y el hombre la ve de lejos.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
He aquí que Dios es grande, y nosotros no le conoceremos: ni se puede rastrear el número de sus años.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Porque él detiene las goteras de las aguas, cuando la lluvia se derrama de su vapor.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Cuando gotean de las nubes, gotean sobre los hombres en abundancia.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
¿Si entenderá también los extendimientos de las nubes, y los bramidos de su tabernáculo?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
He aquí, que él extendió sobre ella su luz; y cubrió las raíces de la mar.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Con ellas castiga a los pueblos, y da comida a la multitud.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Con las nubes encubre la luz, y les manda que vayan contra ella.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
La una da nuevas de la otra: la una adquiere ira contra la que viene.

< Ayuba 36 >