< Ayuba 36 >
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Espérame un poco y te diré más, porque aún queda algo por decir en defensa de ʼEloha.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Desde lejos traeré mi saber y atribuiré justicia a mi Hacedor,
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
porque en verdad mis palabras no son falsas. Contigo está Uno que es perfecto en conocimiento.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Ciertamente ʼEL es poderoso, pero no desprecia a nadie. Es poderoso en la fuerza del entendimiento.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
No otorga vida al perverso, pero hace justicia a los afligidos.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
No aparta sus ojos de los justos. Los hace sentar con reyes en el trono para siempre, y serán exaltados.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Si están presos con grilletes y atrapados con cuerdas de aflicción,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
los reprende por su obra y por sus transgresiones, porque se exaltaron a sí mismos.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Les abre el oído a la corrección y los exhorta a devolverse de la iniquidad.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Si escuchan y se someten, acaban sus días en prosperidad, y sus años en deleites.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Pero si no escuchan, perecen a filo de espada o por su ignorancia.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Los impíos de corazón atesoran ira, no claman cuando Él los ata y
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
mueren en la juventud. Sus vidas terminan entre los sodomitas con rituales paganos.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Él libra a los afligidos en su aflicción. Abre sus oídos en la opresión.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
También te sacará de las garras de la angustia a un lugar espacioso y abierto, para servirte una mesa llena de sustancia.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Pero si tú estás lleno del juicio que merece el perverso, el juicio y la justicia se apoderan de ti.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Por lo cual, teme, no sea que en su ira te quite de un golpe, del cual no te pueda librar ni un gran rescate.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
¿Será suficiente tu clamor para librarte de la angustia o todas las fuerzas de tu poder?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
No anheles la noche en la cual los pueblos desaparecerán de su lugar.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Cuídate de no volver a la iniquidad, porque escogiste ésta en vez de la aflicción.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Ciertamente ʼEL es exaltado en su poder: ¿Quién es un Maestro como Él?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
¿Quién le señala el camino? ¿Quién le dirá jamás: Cometiste injusticia?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Acuérdate de engrandecer su obra, de la cual los hombres cantan.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Todos los hombres la contemplan. Los humanos la miran desde lejos.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Mira, ʼEL es exaltado, y nosotros no lo conocemos. El número de sus años es inescrutable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Él atrae las gotas de agua, y a la lluvia convierte en vapor
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
que destilan las nubes, y vierten en abundancia sobre los hombres.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
¿Quién entenderá el despliegue de las nubes y el estruendo de la bóveda celeste?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Ciertamente, despliega su rayo en ella y cubre las profundidades del mar.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Con tales cosas gobierna a los pueblos y da alimento en abundancia.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Cubre con sus manos el rayo y lo lanza certero hacia su blanco.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
El trueno anuncia su presencia, el ganado también, con respecto a la tormenta que se levanta.