< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Proseguiu ainda Elihu, e disse:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Espera-me um pouco, e mostrar-te-ei que ainda há razões a favor de Deus.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Desde longe repetirei a minha opinião; e ao meu criador atribuirei a justiça.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Porque na verdade, as minhas palavras não serão falsas: contigo está um que é sincero na sua opinião.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Eis que Deus é mui grande, contudo a ninguém despreza: grande é em força de coração.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Não deixa viver ao ímpio, e faz justiça aos aflitos.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Do justo não tira os seus olhos; antes estão com os reis no trono; ali os assenta para sempre, e assim são exaltados.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
E, se estando presos em grilhões, os detém amarrados com cordas de aflição,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Então lhes faz saber a obra deles, e as suas transgressões; porquanto prevaleceram nelas.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
E revela-lho aos seus ouvidos, para seu ensino; e diz-lhes que se convertam da maldade.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Se o ouvirem, e o servirem, acabarão seus dias em bem, e os seus anos em delícias.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Porém se o não ouvirem, à espada os passarão, e expirarão sem conhecimento.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
E os hipócritas de coração amontoam para si a ira; e amarrando-os ele, não clamam por socorro.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
A sua alma morre na mocidade, e a sua vida entre os sodomitas.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Ao aflito livra, da sua aflição, e na opressão o revelará aos seus ouvidos.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Assim também te desviará da boca da angústia para um lugar espaçoso, em que não haja aperto, e as iguarias da tua mesa serão cheias de gordura.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
E estarás satisfeito com o juízo do ímpio: o juízo e a justiça te sustentarão.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Porquanto há furor, guarda-te de que porventura te não tire de pancada, pois por grande preço te não poderiam retirar dali.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Estimaria ele tanto tuas riquezas, ou alguns esforços da força, que por isso não estivesses em aperto?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Não suspires pela noite, em que os povos sejam tomados do seu lugar.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Guarda-te, e não declines para a iniquidade: porquanto nisto a escolheste, por causa da tua miséria.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Eis que Deus exalta com a sua força; quem ensina como ele?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Quem lhe pedirá conta do seu caminho? ou, quem lhe disse: Tu cometeste maldade?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Lembra-te de que engrandeças a sua obra que os homens contemplam.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Todos os homens a veem, e o homem a enxerga de longe.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Eis que Deus é grande, e nós o não compreendemos, e o número dos seus anos se não pode esquadrinhar.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Porque faz miúdas as gotas das águas que derramam a chuva do seu vapor.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
A qual as nuvens destilam e gotejam sobre o homem abundantemente.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Porventura também se poderão entender as extensões das nuvens, e os estalos da sua tenda?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Eis que estende sobre elas a sua luz, e encobre os altos do mar.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Porque por estas coisas julga os povos e lhes dá mantimento em abundância.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Com as mãos encobre a luz, e faz-lhe proibição pela que passa por entre elas.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
O que dá a entender o seu pensamento, como também aos gados, acerca do temporal que sobe.

< Ayuba 36 >