< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
و الیهو باز‌گفت:۱
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
«برای من‌اندکی صبرکن تا تو را اعلام نمایم، زیرا از برای خدا هنوز سخنی باقی است.۲
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
علم خود را از دورخواهم آورد و به خالق خویش، عدالت راتوصیف خواهم نمود.۳
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
چونکه حقیقت کلام من دروغ نیست، و آنکه در علم کامل است نزد توحاضر است.۴
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
اینک خدا قدیر است و کسی رااهانت نمی کند و در قوت عقل قادر است.۵
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
شریررا زنده نگاه نمی دارد و داد مسکینان را می‌دهد.۶
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
چشمان خود را از عادلان برنمی گرداند، بلکه ایشان را با پادشاهان بر کرسی تا به ابد می‌نشاند، پس سرافراشته می‌شوند.۷
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
اما هرگاه به زنجیرهابسته شوند، و به بندهای مصیبت گرفتار گردند،۸
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
آنگاه اعمال ایشان را به ایشان می‌نمایاند وتقصیرهای ایشان را از اینکه تکبر نموده‌اند،۹
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
وگوشهای ایشان را برای تادیب باز می‌کند، و امرمی فرماید تا از گناه بازگشت نمایند.۱۰
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
پس اگربشنوند و او را عبادت نمایند، ایام خویش را درسعادت بسر خواهند برد، و سالهای خود را درشادمانی.۱۱
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
و اما اگر نشنوند از تیغ خواهند افتاد، و بدون معرفت، جان را خواهند سپرد.۱۲
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
اماآنانی که در دل، فاجرند غضب را ذخیره می‌نمایند، و چون ایشان را می‌بندد استغاثه نمی نمایند.۱۳
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
ایشان در عنفوان جوانی می‌میرندو حیات ایشان با فاسقان (تلف می‌شود).۱۴
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
مصیبت کشان را به مصیبت ایشان نجات می‌بخشد و گوش ایشان را در تنگی باز می‌کند.۱۵
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
«پس تو را نیز از دهان مصیبت بیرون می‌آورد، در مکان وسیع که در آن تنگی نمی بود وزاد سفره تو از فربهی مملو می‌شد،۱۶
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
و تو ازداوری شریر پر هستی، لیکن داوری و انصاف باهم ملتصقند.۱۷
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
باحذر باش مبادا خشم تو را به تعدی ببرد، و زیادتی کفاره تو را منحرف سازد.۱۸
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
آیا او دولت تو را به حساب خواهد آورد؟ نی، نه طلا و نه تمامی قوای توانگری را.۱۹
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
برای شب آرزومند مباش، که امت‌ها را از جای ایشان می‌برد.۲۰
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
با حذر باش که به گناه مایل نشوی، زیرا که تو آن را بر مصیبت ترجیح داده‌ای.۲۱
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
اینک خدا در قوت خود متعال می‌باشد. کیست که مثل او تعلیم بدهد؟۲۲
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
کیست که طریق او را به او تفویض کرده باشد؟ و کیست که بگویدتو بی‌انصافی نموده‌ای؟۲۳
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
به یاد داشته باش که اعمال او را تکبیر گویی که درباره آنها مردمان می‌سرایند.۲۴
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
جمیع آدمیان به آنها می‌نگرند. مردمان آنها را از دور مشاهده می‌نمایند.۲۵
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
اینک خدا متعال است و او را نمی شناسیم. و شماره سالهای او را تفحص نتوان کرد.۲۶
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
زیرا که قطره های آب را جذب می‌کند و آنها باران را ازبخارات آن می‌چکاند.۲۷
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
که ابرها آن را به شدت می‌ریزد و بر انسان به فراوانی می‌تراود.۲۸
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
آیاکیست که بفهمد ابرها چگونه پهن می‌شوند، یارعدهای خیمه او را بداند؟۲۹
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
اینک نور خود رابر آن می‌گستراند. و عمق های دریا را می‌پوشاند.۳۰
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
زیرا که به واسطه آنها قوم‌ها را داوری می‌کند، و رزق را به فراوانی می‌بخشد.۳۱
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
دستهای خودرا با برق می‌پوشاند، و آن را بر هدف مامورمی سازد.۳۲
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
رعدش از او خبر می‌دهد و مواشی از برآمدن او اطلاع می‌دهند.۳۳

< Ayuba 36 >