< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Addens quoque Eliu, hæc locutus est:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Sustine me paululum, et indicabo tibi: adhuc enim habeo quod pro Deo loquar.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Repetam scientiam meam a principio, et operatorem meum probabo iustum.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Vere enim absque mendacio sermones mei, et perfecta scientia probabitur tibi.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Deus potentes non abiicit, cum et ipse sit potens.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Sed non salvat impios, et iudicium pauperibus tribuit.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Non auferet a iusto oculos suos, et reges in solio collocat in perpetuum, et illi eriguntur.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Et si fuerint in catenis, et vinciantur funibus paupertatis.
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Indicabit eis opera eorum, et scelera eorum, quia violenti fuerunt.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Revelabit quoque aurem eorum, ut corripiat: et loquetur, ut revertantur ab iniquitate.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Si audierint et observaverint, complebunt dies suos in bono, et annos suos in gloria:
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Si autem non audierint, transibunt per gladium, et consumentur in stultitia.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Simulatores et callidi provocant iram Dei, neque clamabunt cum vincti fuerint.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Morietur in tempestate anima eorum, et vita eorum inter effeminatos.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Eripiet de angustia sua pauperem, et revelabit in tribulatione aurem eius.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Igitur salvabit te de ore angusto latissime, et non habente fundamentum subter se: requies autem mensæ tuæ erit plena pinguedine.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Causa tua quasi impii iudicata est, causam iudiciumque recipies.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Non te ergo superet ira, ut aliquem opprimas: nec multitudo donorum inclinet te.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Depone magnitudinem tuam absque tribulatione, et omnes robustos fortitudine.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Ne protrahas noctem, ut ascendant populi pro eis.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Cave ne declines ad iniquitatem: hanc enim cœpisti sequi post miseriam.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Ecce, Deus excelsus in fortitudine sua, et nullus ei similis in legislatoribus.
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Quis poterit scrutari vias eius? aut quis potest ei dicere: Operatus es iniquitatem?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Memento quod ignores opus eius, de quo cecinerunt viri.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Omnes homines vident eum, unusquisque intuetur procul.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Ecce, Deus magnus vincens scientiam nostram: numerus annorum eius inæstimabilis.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Qui aufert stillas pluviæ, et effundit imbres ad instar gurgitum.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Qui de nubibus fluunt, quæ prætexunt cuncta desuper.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Si voluerit extendere nubes quasi tentorium suum,
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Et fulgurare lumine suo desuper, cardines quoque maris operiet.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Per hæc enim iudicat populos, et dat escas multis mortalibus.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
In manibus abscondit lucem, et præcepit ei ut rursus adveniat.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Annunciat de ea amico suo, quod possessio eius sit, et ad eam possit ascendere.

< Ayuba 36 >