< Ayuba 36 >
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
「しばらく待て、わたしはあなたに示すことがある。なお神のために言うべき事がある。
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
わたしは遠くからわが知識を取り、わが造り主に正義を帰する。
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
まことにわたしの言葉は偽らない。知識の全き者があなたと共にいる。
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
見よ、神は力ある者であるが、何をも卑しめられない、その悟りの力は大きい。
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
彼は悪しき者を生かしておかれない、苦しむ者のためにさばきを行われる。
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
彼は正しい者から目を離さず、位にある王たちと共に、とこしえに、彼らをすわらせて、尊くされる。
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
もし彼らが足かせにつながれ、悩みのなわに捕えられる時は、
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
彼らの行いと、とがと、その高ぶったふるまいを彼らに示し、
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
彼らの耳を開いて、教を聞かせ、悪を離れて帰ることを命じられる。
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
もし彼らが聞いて彼に仕えるならば、彼らはその日を幸福に過ごし、その年を楽しく送るであろう。
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
しかし彼らが聞かないならば、つるぎによって滅び、知識を得ないで死ぬであろう。
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
心に神を信じない者どもは怒りをたくわえ、神に縛られる時も、助けを呼び求めることをしない。
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
彼らは年若くして死に、その命は恥のうちに終る。
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
神は苦しむ者をその苦しみによって救い、彼らの耳を逆境によって開かれる。
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
神はまたあなたを悩みから、束縛のない広い所に誘い出された。そしてあなたの食卓に置かれた物はすべて肥えた物であった。
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
しかしあなたは悪人のうくべきさばきをおのれに満たし、さばきと公義はあなたを捕えている。
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
あなたは怒りに誘われて、あざけりに陥らぬように心せよ。あがないしろの大いなるがために、おのれを誤るな。
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
あなたの叫びはあなたを守って、悩みを免れさせるであろうか、いかに力をつくしても役に立たない。
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
人々がその所から断たれるその夜を慕ってはならない。
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
慎んで悪に傾いてはならない。あなたは悩みよりもむしろこれを選んだからだ。
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
見よ、神はその力をもってあがめられる。だれか彼のように教える者があるか。
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
だれか彼のためにその道を定めた者があるか。だれか『あなたは悪い事をした』と言いうる者があるか。
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
神のみわざをほめたたえる事を忘れてはならない。これは人々の歌いあがめるところである。
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
すべての人はこれを仰ぎ見る。人は遠くからこれを見るにすぎない。
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
見よ、神は大いなる者にいまして、われわれは彼を知らない。その年の数も計り知ることができない。
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
彼は水のしたたりを引きあげ、その霧をしたたらせて雨とされる。
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
空はこれを降らせて、人の上に豊かに注ぐ。
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
だれか雲の広がるわけと、その幕屋のとどろくわけとを悟ることができようか。
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
見よ、彼はその光をおのれのまわりにひろげ、また海の底をおおわれる。
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
彼はこれらをもって民をさばき、食物を豊かに賜い、
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
いなずまをもってもろ手を包み、これに命じて敵を打たせられる。
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
そのとどろきは、悪にむかって怒りに燃える彼を現す。