< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
ויסף אליהוא ויאמר
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
כתר-לי זעיר ואחוך כי עוד לאלוה מלים
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
אשא דעי למרחוק ולפעלי אתן-צדק
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
כי-אמנם לא-שקר מלי תמים דעות עמך
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
הן-אל כביר ולא ימאס כביר כח לב
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
לא-יחיה רשע ומשפט עניים יתן
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
לא-יגרע מצדיק עיניו ואת-מלכים לכסא וישיבם לנצח ויגבהו
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
ואם-אסורים בזקים ילכדון בחבלי-עני
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
ויגד להם פעלם ופשעיהם כי יתגברו
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
ויגל אזנם למוסר ויאמר כי-ישובון מאון
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
אם-ישמעו ויעבדו יכלו ימיהם בטוב ושניהם בנעימים
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
ואם-לא ישמעו בשלח יעברו ויגועו בבלי-דעת
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
וחנפי-לב ישימו אף לא ישועו כי אסרם
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
תמת בנער נפשם וחיתם בקדשים
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
יחלץ עני בעניו ויגל בלחץ אזנם
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
ואף הסיתך מפי-צר-- רחב לא-מוצק תחתיה ונחת שלחנך מלא דשן
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
ודין-רשע מלאת דין ומשפט יתמכו
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
כי-חמה פן-יסיתך בספק ורב-כפר אל-יטך
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
היערך שועך לא בצר וכל מאמצי-כח
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
אל-תשאף הלילה-- לעלות עמים תחתם
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
השמר אל-תפן אל-און כי-על-זה בחרת מעני
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
הן-אל ישגיב בכחו מי כמהו מורה
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
מי-פקד עליו דרכו ומי-אמר פעלת עולה
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
זכר כי-תשגיא פעלו-- אשר שררו אנשים
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
כל-אדם חזו-בו אנוש יביט מרחוק
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
הן-אל שגיא ולא נדע מספר שניו ולא-חקר
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
כי יגרע נטפי-מים יזקו מטר לאדו
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
אשר-יזלו שחקים ירעפו עלי אדם רב
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
אף אם-יבין מפרשי-עב תשאות סכתו
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
הן-פרש עליו אורו ושרשי הים כסה
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
כי-בם ידין עמים יתן-אכל למכביר
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
על-כפים כסה-אור ויצו עליה במפגיע
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
יגיד עליו רעו מקנה אף על-עולה

< Ayuba 36 >