< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Weiter fuhr Elihu also fort:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Warte mir ein wenig, daß ich dich unterweise, denn noch stehen Gott Worte zu Gebote.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Ich will mein Wissen fernher entnehmen und meinem Schöpfer Recht verschaffen.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Denn wahrlich, meine Worte lügen nicht; mit einem Manne von vollkommener Erkenntnis hast du's zu thun.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Siehe, Gott ist gewaltig, doch verschmäht er niemand, gewaltig an Kraft des Geistes.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Er erhält den Gottlosen nicht am Leben, aber den Elenden gewährt er Recht.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Er zieht seine Augen nicht ab von dem Frommen und bei Königen auf dem Thron - da läßt er sie immerdar sitzen, daß sie erhöht seien.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Und wenn sie mit Ketten gebunden sind, gefangen gehalten werden von Stricken des Elends,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
und er ihnen ihr Thun vorhält und ihre Sünden, daß sie sich überhoben,
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
und er so ihr Ohr der Warnung aufthut und sie umkehren heißt vom Frevel:
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Wenn sie gehorchen und sich unterwerfen, so werden sie ihre Tage im Glück und ihre Jahre in Wonne verbringen.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Gehorchen sie aber nicht, so fahren sie dahin durch Geschosse und verhauchen in Verblendung.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Denn als Leute von ruchlosem Sinn hegen sie Zorn, schreien nicht, wenn er sie fesselt;
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
in der Jugendfrische stirbt ihre Seele dahin, und ihr Leben wie das der Lustbuben.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Erretten wird er den Elenden durch sein Elend und thut ihnen durch die Drangsal das Ohr auf.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Und er lockt auch dich aus dem Rachen der Not auf weiten Plan, wo keine Beengung ist, und was auf deinen Tisch kommt, ist reich an Fett.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Bist du aber erfüllt vom Urteile des Gottlosen, so werden Urteil und Gericht dich festhalten.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Denn Grimm verführe dich nicht zu Hohn, und des Lösegelds Größe verleite dich nicht.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Wird er deinem Schreien anders abhelfen, als durch Bedrängnis und alle Kraftanstrengungen?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Lechze nicht nach der Nacht, daß Völker auffahren an ihrer Stelle,
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Hüte dich, wende dich nicht zum Frevel; denn dazu hast du mehr Lust als zum Leiden.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Siehe, Gott wirkt erhaben in seiner Kraft; wer ist ein Herrscher wie er?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Wer hat ihm seinen Weg vorgeschrieben, und wer gesagt: du hast Unrecht gethan?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Gedenke, daß du sein Thun erhebst, welches die Menschen besingen!
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Alle Menschen schauen ihre Lust daran; der Sterbliche erblickt es von ferne.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Ja, Gott ist erhaben und unbegreiflich für uns, die Zahl seiner Jahre nicht zu erforschen.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Denn er zählt des Wassers Tropfen ab, daß sie infolge seines Nebels Regen sickern,
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
den die Wolken rieseln lassen, auf viele Menschen niederträufeln.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Und vollends, wenn man die Ausbreitungen des Gewölks verstände, das Krachen seines Gezelts!
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Siehe, er breitet um sich aus sein Licht und bedeckt die Wurzeln des Meers.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Denn damit richtet er Völker, giebt Speise zugleich im Überfluß.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Beide Hände bedeckt er mit Licht und entbietet es gegen den Widersacher.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Ihn meldet an sein Dröhnen, ihn, der seinen Zorn gegen das Unrecht eifern laßt.

< Ayuba 36 >