< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu continua [de parler], et dit:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Attends-moi un peu, et je te montrerai qu'il y a encore d'autres raisons pour la cause de Dieu.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Je tirerai de loin mes raisons, et je défendrai la justice de celui qui m'a fait.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Car certainement il n'y aura rien de faux en tout ce que je dirai, et celui qui est avec toi, est infaillible dans ses raisons.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Voilà, Dieu est plein de force, mais il ne dédaigne personne, encore qu'il soit puissant de force de cœur.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Il ne laisse point vivre le méchant, et il fait justice aux affligés.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Il ne retire point ses yeux de dessus le juste, même [il place les justes] sur le trône avec les Rois, et les [y] fait asseoir pour toujours, et ils sont élevés.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Que s'ils sont liés de chaînes, et s'ils sont prisonniers dans les liens de l'affliction,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Il leur montre ce qu'ils ont fait, et il [leur fait connaître] que leurs péchés se sont augmentés.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Alors il leur ouvre l'oreille pour les rendre sages; et il leur dit, qu'ils se détournent de l'iniquité.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
S'ils l'écoutent, et le servent, ils achèveront heureusement leurs jours, et leurs années dans les plaisirs;
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mais s'ils n'écoutent point, ils passeront par le fil de l'épée, et ils expireront pour n'avoir pas été sages.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Et ceux qui sont hypocrites en leur cœur, attirent sur eux la colère; ils ne crieront point quand il les aura liés.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Leur personne mourra étant encore dans sa vigueur; et leur vie finira parmi ceux qui se prostituent à la paillardise.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
[Mais] il tire l'affligé hors de son affliction, et il lui ouvre l'oreille dans l'oppression.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
C'est pourquoi il t'eût tiré hors de l'angoisse, pour te mettre au large, il n'y eût eu rien qui t'eût serré, et ta table eût été toute couverte de viandes grasses.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Or tu as rempli le jugement du méchant, mais le jugement et le droit subsisteront.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Certainement [Dieu] est irrité; prends garde qu'il ne te plonge dans l'affliction, car il n'y aura point alors de rançon si grande, qu'elle puisse te délivrer.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Ferait-il quelque cas de tes richesses? il ne ferait aucun cas ni de ton or, ni de toute ta grande puissance.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Ne soupire point après la nuit en laquelle les peuples s'évanouissent de leur place;
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Et garde-toi de retourner à l'iniquité; car tu en as fait le choix, pour t'être affligé comme tu as fait.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Voici, le [Dieu] Fort élève les hommes par sa puissance; [et] qui est-ce qui enseignerait comme lui?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Qui est-ce qui lui a prescrit le chemin qu'il devait tenir? et qui lui a dit: Tu as fait une injustice?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Souviens-toi de célébrer son ouvrage, que les hommes voient.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Tout homme le voit, chacun l'aperçoit de loin.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Voici, le [Dieu] Fort est grand, et nous ne le connaissons point; et quant au nombre de ses années, on ne le peut sonder.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Parce qu'il met les eaux en petites gouttes, elles répandent la pluie selon la vapeur qui la contient.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Et les nuées la font distiller et dégoutter sur les hommes en abondance.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Et qui pourrait comprendre la [grande] étendue de la nuée, et le son éclatant de son tabernacle?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Voilà, il étend sa lumière sur elle, et il couvre le fond de la mer.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Or c'est par ces choses-là qu'il juge les peuples, [et] qu'il donne des vivres en abondance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Il tient caché dans les paumes de ses mains le feu étincelant, et il lui donne ses ordres à l'égard de ce qui se présente à sa rencontre.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Son bruit en porte les nouvelles, [et] il y a de la fureur contre celle qui monte [à qui gagnera la place].

< Ayuba 36 >