< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Élihu continua et dit:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Attends un peu, et je vais poursuivre, Car j’ai des paroles encore pour la cause de Dieu.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Je prendrai mes raisons de haut, Et je prouverai la justice de mon créateur.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Sois-en sûr, mes discours ne sont pas des mensonges, Mes sentiments devant toi sont sincères.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Dieu est puissant, mais il ne rejette personne; Il est puissant par la force de son intelligence.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Il ne laisse pas vivre le méchant, Et il fait droit aux malheureux.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Il ne détourne pas les yeux de dessus les justes, Il les place sur le trône avec les rois, Il les y fait asseoir pour toujours, afin qu’ils soient élevés.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Viennent-ils à tomber dans les chaînes, Sont-ils pris dans les liens de l’adversité,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Il leur dénonce leurs œuvres, Leurs transgressions, leur orgueil;
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Il les avertit pour leur instruction, Il les exhorte à se détourner de l’iniquité.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
S’ils écoutent et se soumettent, Ils achèvent leurs jours dans le bonheur, Leurs années dans la joie.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
S’ils n’écoutent pas, ils périssent par le glaive, Ils expirent dans leur aveuglement.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Les impies se livrent à la colère, Ils ne crient pas à Dieu quand il les enchaîne;
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Ils perdent la vie dans leur jeunesse, Ils meurent comme les débauchés.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Mais Dieu sauve le malheureux dans sa misère, Et c’est par la souffrance qu’il l’avertit.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Il te retirera aussi de la détresse, Pour te mettre au large, en pleine liberté, Et ta table sera chargée de mets succulents.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Mais si tu défends ta cause comme un impie, Le châtiment est inséparable de ta cause.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Que l’irritation ne t’entraîne pas à la moquerie, Et que la grandeur de la rançon ne te fasse pas dévier!
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Tes cris suffiraient-ils pour te sortir d’angoisse, Et même toutes les forces que tu pourrais déployer?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Ne soupire pas après la nuit, Qui enlève les peuples de leur place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Garde-toi de te livrer au mal, Car la souffrance t’y dispose.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Dieu est grand par sa puissance; Qui saurait enseigner comme lui?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Qui lui prescrit ses voies? Qui ose dire: Tu fais mal?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Souviens-toi d’exalter ses œuvres, Que célèbrent tous les hommes.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Tout homme les contemple, Chacun les voit de loin.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Dieu est grand, mais sa grandeur nous échappe, Le nombre de ses années est impénétrable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Il attire à lui les gouttes d’eau, Il les réduit en vapeur et forme la pluie;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Les nuages la laissent couler, Ils la répandent sur la foule des hommes.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Et qui comprendra le déchirement de la nuée, Le fracas de sa tente?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Voici, il étend autour de lui sa lumière, Et il se cache jusque dans les profondeurs de la mer.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Par ces moyens il juge les peuples, Et il donne la nourriture avec abondance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Il prend la lumière dans sa main, Il la dirige sur ses adversaires.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Il s’annonce par un grondement; Les troupeaux pressentent son approche.

< Ayuba 36 >