< Ayuba 36 >
Éliu reprit encore une fois et dit:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Attends un peu, et je t’instruirai, car j’ai des paroles encore pour la cause de Dieu;
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
je prendrai mes raisons de haut, et je montrerai la justice de mon Créateur.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Sois-en sûr, mes discours sont exempts de mensonge; devant toi est un homme sincère en ses jugements.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Voici que Dieu est puissant, mais il ne dédaigne personne; il est puissant par la force de son intelligence.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Il ne laisse pas vivre le méchant, et il fait justice aux malheureux.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
Il ne détourne pas ses yeux des justes; il les fait asseoir sur le trône avec les rois, il les établit pour toujours, et ils sont exaltés.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Viennent-ils à tomber dans les fers, sont-ils pris dans les liens du malheur,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
il leur dénonce leurs œuvres, leurs fautes causées par l’orgueil.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Il ouvre leur oreille à la réprimande, il les exhorte à se détourner du mal.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
S’ils écoutent et se soumettent, ils achèvent leurs jours dans le bonheur, et leurs années dans les délices.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Mais s’ils n’écoutent pas, ils périssent par le glaive, ils meurent dans leur aveuglement.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Les cœurs impies se livrent à la colère, ils ne crient pas vers Dieu quand il les met dans les chaînes.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Aussi meurent-ils dans leur jeunesse, et leur vie se flétrit comme celle des infâmes.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Mais Dieu sauve le malheureux dans sa misère, il l’instruit par la souffrance.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Toi aussi, il te retirera de la détresse, pour te mettre au large, en pleine liberté, et ta table sera dressée et chargée de mets succulents.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Mais si tu combles la mesure de l’impie, tu en porteras la sentence et la peine.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Crains que Dieu irrité ne t’inflige un châtiment, et que tes riches offrandes ne t’égarent.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Tes cris te tireront-ils de la détresse, et même toutes les ressources de la force?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Ne soupire pas après la nuit, durant laquelle les peuples sont anéantis sur place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Prends garde de te tourner vers l’iniquité, car tu la préfères à l’affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Vois: Dieu est sublime dans sa puissance! Quel maître est semblable à lui?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Qui lui trace la voie qu’il doit suivre? Qui peut lui dire: « Tu as mal fait? »
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Songe plutôt à glorifier ses œuvres, que les hommes célèbrent dans leurs chants.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Tout homme les admire, le mortel les contemple de loin.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Dieu est grand au-dessus de toute science, le nombre de ses années est impénétrable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Il attire les gouttes d’eau, qui se répandent en pluie sous leur poids.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Les nuées la laissent couler, et tomber sur la masse des hommes.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Qui comprendra l’expansion des nuages, et le fracas de la tente du Très-Haut?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Tantôt il étend autour de lui sa lumière, tantôt il se cache comme au fond de la mer.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
C’est ainsi qu’il exerce sa justice sur les peuples, et qu’il donne la nourriture avec abondance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Il prend la lumière dans ses mains, et lui marque le but à atteindre.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Son tonnerre l’annonce, l’effroi des troupeaux annonce son approche.