< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu also continued, and said,
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
“Bear with me a little, and I will show you; for I still have something to say on God’s behalf.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will get my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For truly my words are not false. One who is perfect in knowledge is with you.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
“Behold, God is mighty, and doesn’t despise anyone. He is mighty in strength of understanding.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He doesn’t preserve the life of the wicked, but gives justice to the afflicted.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He doesn’t withdraw his eyes from the righteous, but with kings on the throne, he sets them forever, and they are exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
If they are bound in fetters, and are taken in the cords of afflictions,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
then he shows them their work, and their transgressions, that they have behaved themselves proudly.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He also opens their ears to instruction, and commands that they return from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they listen and serve him, they will spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they don’t listen, they will perish by the sword; they will die without knowledge.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
“But those who are godless in heart lay up anger. They don’t cry for help when he binds them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die in youth. Their life perishes among the unclean.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
He delivers the afflicted by their affliction, and opens their ear in oppression.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Yes, he would have allured you out of distress, into a wide place, where there is no restriction. That which is set on your table would be full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
“But you are full of the judgment of the wicked. Judgment and justice take hold of you.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Don’t let riches entice you to wrath, neither let the great size of a bribe turn you aside.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Would your wealth sustain you in distress, or all the might of your strength?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Don’t desire the night, when people are cut off in their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Take heed, don’t regard iniquity; for you have chosen this rather than affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Behold, God is exalted in his power. Who is a teacher like him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who has prescribed his way for him? Or who can say, ‘You have committed unrighteousness’?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
“Remember that you magnify his work, about which men have sung.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
All men have looked on it. Man sees it afar off.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Behold, God is great, and we don’t know him. The number of his years is unsearchable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
For he draws up the drops of water, which distill in rain from his vapor,
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
which the skies pour down and which drop on man abundantly.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Indeed, can anyone understand the spreading of the clouds and the thunderings of his pavilion?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Behold, he spreads his light around him. He covers the bottom of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
For by these he judges the people. He gives food in abundance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
He covers his hands with the lightning, and commands it to strike the mark.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Its noise tells about him, and the livestock also, concerning the storm that comes up.

< Ayuba 36 >