< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu [finished by] saying this:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
“[Job, ] be patient with me a little longer, because I have something else to teach you. I have something else to say that God [wants you to know].
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will tell you what I have learned from many sources, in order to show that God, my creator, is just/fair.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
I am not saying anything to you that is false; I, who am standing in front of you, am someone who understands things (very well/perfectly) [HYP].
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
“Hey, God is [very] powerful, and he does not despise anyone, and he understands everything.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He does not allow wicked people to remain alive, and he always acts justly toward those who are poor.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He always watches over [MTY] those who are righteous; he allows them to sit on thrones [and rule] with kings, and they are honored forever.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
But if people [who commit crimes] are caught, they [are thrown into prison and] are caused to suffer by being fastened with chains.
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
When that happens, God shows them what they have done; he shows them the sins that they have committed, and he shows them that they have been proud/arrogant.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He causes them to listen [MTY] to what he is warning them, and he commands them to turn away from [doing what is] evil.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they (listen to/heed) him and serve him, [after they get out of prison] they will prosper for all the years that they are alive and be peaceful/happy.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they do not (listen/pay attention) to him, they will die violently, not knowing [why God is causing them to die].
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
“Godless/Wicked people continue being angry, and they do not cry out for help, [even] when God is punishing them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die while they are still young, disgraced because of their very immoral behavior [EUP].
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
But God teaches people by causing them to suffer; by afflicting them, he causes them to listen to [MTY] what he is telling them.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
“And Job, [I think that] God [wants to] bring you out of your troubles and allow you to live without distress; he wants your table to be full of very nice food.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But now, you are being punished [MTY] as wicked people are punished; [God] [PRS] has been punishing you (justly/as you deserve).
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
So be careful that you are not deceived by [desiring to acquire] money or that you are not ruined by [accepting] large bribes.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
[If you are deceived by those things, ] it certainly will not [RHQ] help you to cry out when you are distressed; all of your strength will not help you.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Do not wish that it would be nighttime [in order that God will not see you and punish you], because night is the time when [even] people-groups are destroyed!
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Be careful not to [begin doing] evil things, because [God] has caused you to suffer to prevent you from doing evil.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
“Hey, God is extremely powerful; there is certainly [RHQ] no teacher who teaches like he does.
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
No one has [RHQ] told him what he should do, and no one has [RHQ] said to him, ‘You have done what is wrong!’
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
People have [always] sung to praise him, so you also should never forget to praise him for what he has done.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Everyone has seen [what he has done], but [sometimes] we can see it only from far away.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
“Hey, God is very great, and we are not able to know how great he is, and we do not know how old he is.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
He draws water up [from the earth and puts it in clouds] and causes it to become rain.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
The rain pours down from the sky/clouds; God causes abundant showers to fall on everyone.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
No one can [RHQ] understand how the clouds move [across the sky] or how it thunders in the sky where God lives.
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
He causes lightning to flash all around him, but he causes the bottom of the oceans to remain dark.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
By providing plenty of rain for us, he enables us to have abundant food.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
[It is as though] he holds the lightning in his hands, and [then] he commands it to strike where he wants it to.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
When we hear his thunder, we know that there will be a storm, and the cattle know it, too.”

< Ayuba 36 >