< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
And Elihu added and said: —
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Restrain thyself for me a little, and I will shew thee, that, yet—for GOD, there is justification,
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will bring my knowledge from afar, and, to my Maker, will I attribute righteousness.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For, of a truth—not false, are my words, One of competent knowledge, is with thee.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Lo! GOD, is mighty, yet will he not despise, Mighty in vigour of mind;
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He will not keep alive one who is lawless, but, the right of oppressed ones, will he grant;
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He will not withdraw—from a righteous one—his eyes, —but, with kings on the throne, He hath seated men triumphantly, and they have been exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
But, if, bound in fetters, they have been captured with cords of affliction,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Then hath he declared to them their deed, and their transgressions—that they were wont to behave themselves proudly;
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Thus hath he uncovered their ear to a warning, and said—that they should turn from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they would hearken, and serve, they should complete their days, in prosperity, and their years, in pleasantness;
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But, if they would not hearken, by a weapon, should they pass away, and breathe their last, no one knowing.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Yea, the impious in heart, should store up anger, They should not cry for help, when he bound them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Their soul should die in youth, and their life, among the unclean.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
He would deliver the humbled in his humiliation, and would uncover—in oppression—their ear.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Yea he might even have allured thee—out of the mouth of straitness, [into] a wide space—no narrowness there, —and, the food set down on thy table, should have been full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But, with the plea of a lawless one, thou art full, Plea and sentence, will take fast hold.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Because there is wrath, [beware] lest he take thee away with a stroke, Then let not, a great ransom, mislead thee.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Will he value thy riches? Nay not precious ore, nor all the forces of strength.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Do not pant for the night, when peoples disappear from their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Beware, do not turn unto iniquity, For, this, thou hast chosen rather than affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Lo, GOD, exalteth himself by his strength, Who like him doth teach?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who enjoined on him his way? and who ever said, Thou hast wrought perversity?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Remember, that thou extol his work, of which men have sung;
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Every son of earth, hath viewed it, Mortal man, looketh at it from afar.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Lo, GOD, is greater than we can know, The number of his years, even past finding out!
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
For he draweth up drops of water, They trickle as rain through his mist;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
With which the clouds flow down, They drop on man in abundance.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
But surely none can understand the burstings of the cloud, the crashing of his pavilion!
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Lo! he hath spread out over it, his lightning, The bed of the sea, hath he covered.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
For, by those things, he executeth judgment on peoples, He giveth food in abundance:
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Upon both hands, he putteth a covering of lightning, and layeth command upon it against an assailant:
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
His rolling thunder telleth concerning him, —The cattle, even, concerning him that is coming up.

< Ayuba 36 >