< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu also proceeded, and said,
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Suffer me a little, and I will shew thee: for I have yet somewhat to say on God’s behalf.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will fetch my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For truly my words are not false: one that is perfect in knowledge is with thee.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Behold, God is mighty, and despiseth not any: he is mighty in strength of understanding.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He preserveth not the life of the wicked: but giveth to the afflicted [their] right.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He withdraweth not his eyes from the righteous: but with kings upon the throne he setteth them for ever, and they are exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
And if they be bound in fetters, and be taken in the cords of affliction;
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Then he sheweth them their work, and their transgressions, that they have behaved themselves proudly.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He openeth also their ear to instruction, and commandeth that they return from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they hearken and serve [him], they shall spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they hearken not, they shall perish by the sword, and they shall die without knowledge.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
But they that are godless in heart lay up anger: they cry not for help when he bindeth them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die in youth, and their life [perisheth] among the unclean.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
He delivereth the afflicted by his affliction, and openeth their ear in oppression.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Yea, he would have led thee away out of distress into a broad place, where there is no straitness; and that which is set on thy table should be full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But thou art full of the judgment of the wicked: judgment and justice take hold [on thee].
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Because there is wrath, beware lest thou be led away by [thy] sufficiency; neither let the greatness of the ransom turn thee aside.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Will thy riches suffice, [that thou be] not in distress, or all the forces of [thy] strength?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Desire not the night, when peoples are cut off in their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Take heed, regard not iniquity: for this hast thou chosen rather than affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Behold, God doeth loftily in his power: who is a teacher like unto him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who hath enjoined him his way? or who can say, Thou hast wrought unrighteousness?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Remember that thou magnify his work, whereof men have sung.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
All men have looked thereon; man beholdeth it afar off.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Behold, God is great, and we know him not; the number of his years is unsearchable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
For he draweth up the drops of water, which distil in rain from his vapour:
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Which the skies pour down and drop upon man abundantly.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Yea, can any understand the spreadings of the clouds, the thunderings of his pavilion?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Behold, he spreadeth his light around him; and he covereth the bottom of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
For by these he judgeth the peoples; he giveth meat in abundance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
He covereth his hands with the lightning; and giveth it a charge that it strike the mark.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
The noise thereof telleth concerning him, the cattle also concerning [the storm] that cometh up.

< Ayuba 36 >