< Ayuba 36 >
Elihu also proceeded, and said:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Bear with me a little while, that I may show thee! For I have yet words in behalf of God.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will bring my knowledge from afar, And assert the justice of my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Truly my words shall not be false: A man of sound knowledge is before thee.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Behold, God is great, but despiseth not any; Great is he in strength of understanding.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He suffereth not the wicked to prosper, But rendereth justice to the oppressed.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He withdraweth not his eyes from the righteous; But establisheth them for ever with kings on the throne, That they may be exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
And if they be bound in fetters, And holden in the cords of affliction,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Then showeth he them their deeds, And how they have set him at defiance by their transgressions;
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He also openeth their ears to admonition, And commandeth them to return from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they obey and serve him, They spend their days in prosperity, And their years in pleasures.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they obey not, they perish by the sword; They die in their own folly.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
The corrupt in heart treasure up wrath; They cry not to God, when he bindeth them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die in their youth; They close their lives with the unclean.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
But he delivereth the poor in their distress; He openeth their ears in affliction.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
He will bring thee also from the jaws of distress To a broad place, where is no straitness; And the provision of thy table shall be full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But if thou art full of the judgment of the wicked, Judgment and justice shall take hold of thee.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
For if wrath be with him, beware lest he take thee away by his stroke, So that a great ransom shall not save thee!
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Will he esteem thy riches? No! neither thy gold, nor all the abundance of thy wealth.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Long not thou for that night To which nations are taken away from their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Take heed, turn not thine eyes to iniquity! For this hast thou chosen rather than affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Behold, God is exalted in his power: Who is a teacher like him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who hath prescribed to him his way? Or who can say to him, “Thou hast done wrong”?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Forget not to magnify his work, Which men celebrate with songs.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
All mankind gaze upon it; Mortals behold it from afar.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Behold, God is great; we cannot know him, Nor search out the number of his years.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
Lo! he draweth up the drops of water, Which distil rain from his vapor;
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
The clouds pour it down, And drop it upon man in abundance.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Who can understand the spreading of his clouds, And the rattling of his pavilion?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Behold, he spreadeth around himself his light, And he clotheth himself with the depths of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
By these he punisheth nations, And by these he giveth food in abundance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
His hands he covereth with lightning; He giveth it commandment against an enemy.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
His thunder maketh him known; Yea, to the herds, as he ascendeth on high.