< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
ELIHU also proceeded, and said,
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
Suffer me a little, and I will shew thee that I have yet to speak on God’s behalf.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will fetch my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For truly my words shall not be false: he that is perfect in knowledge is with thee.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Behold, God is mighty, and despiseth not any: he is mighty in strength and wisdom.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He preserveth not the life of the wicked: but giveth right to the poor.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He withdraweth not his eyes from the righteous: but with kings are they on the throne; yea, he doth establish them for ever, and they are exalted.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
And if they be bound in fetters, and be holden in cords of affliction;
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
Then he sheweth them their work, and their transgressions that they have exceeded.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He openeth also their ear to discipline, and commandeth that they return from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they obey and serve him, they shall spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
But if they obey not, they shall perish by the sword, and they shall die without knowledge.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
But the hypocrites in heart heap up wrath: they cry not when he bindeth them.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die in youth, and their life is among the unclean.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
He delivereth the poor in his affliction, and openeth their ears in oppression.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Even so would he have removed thee out of the strait into a broad place, where there is no straitness; and that which should be set on thy table should be full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But thou hast fulfilled the judgment of the wicked: judgment and justice take hold on thee.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Because there is wrath, beware lest he take thee away with his stroke: then a great ransom cannot deliver thee.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Will he esteem thy riches? no, not gold, nor all the forces of strength.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Desire not the night, when people are cut off in their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Take heed, regard not iniquity: for this hast thou chosen rather than affliction.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Behold, God exalteth by his power: who teacheth like him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who hath enjoined him his way? or who can say, Thou hast wrought iniquity?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Remember that thou magnify his work, which men behold.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
Every man may see it; man may behold it afar off.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Behold, God is great, and we know him not, neither can the number of his years be searched out.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
For he maketh small the drops of water: they pour down rain according to the vapour thereof:
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Which the clouds do drop and distil upon man abundantly.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Also can any understand the spreadings of the clouds, or the noise of his tabernacle?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Behold, he spreadeth his light upon it, and covereth the bottom of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
For by them judgeth he the people; he giveth meat in abundance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
With clouds he covereth the light; and commandeth it not to shine by the cloud that cometh betwixt.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
The noise thereof sheweth concerning it, the cattle also concerning the vapour.

< Ayuba 36 >