< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu nastavi i reče:
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
“Strpi se malo, pa ću te poučit', jer još nisam sve rekao za Boga.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
Izdaleka ću svoje iznijet' znanje da Stvoritelja svojega opravdam.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Zaista, za laž ne znaju mi riječi, uza te je čovjek znanjem savršen.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
Gle, Bog je silan, ali ne prezire, silan je snagom razuma svojega.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
Opakome on živjeti ne daje, nevoljnicima pravicu pribavlja.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
S pravednika on očiju ne skida, na prijestolje ih diže uz kraljeve da bi dovijeka bili uzvišeni.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
Ako su negvam' oni okovani i užetima nevolje sputani,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
djela njihova on im napominje, kazuje im grijeh njine oholosti.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
Tad im otvara uho k opomeni i poziva ih da se zla okane.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
Poslušaju li te mu se pokore, dani im završavaju u sreći, u užicima godine njihove.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
Ne slušaju li, od koplja umiru, zaglave, sami ne znajući kako.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
A srca opaka mržnju njeguju, ne ištu pomoć kad ih on okuje;
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
u cvatu svoga dječaštva umiru i venu poput hramskih milosnika.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
Nevoljnog on bijedom njegovom spasava i u nesreći otvara mu oči:
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
izbavit će te iz ždrijela tjeskobe k prostranstvima bezgraničnim izvesti, k prepunu stolu mesa pretiloga.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
Ako sudio nisi opakima, ako si pravo krnjio siroti,
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
nek' te obilje odsad ne zavede i nek' te dar prebogat ne iskvari.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Nek' ti je gavan k'o čovjek bez zlata, a čovjek jake ruke poput slaba.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Ne goni one koji su ti tuđi da rodbinu na njino mjesto staviš.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Pazi se da u nepravdu ne skreneš, jer zbog nje snađe tebe iskušenje.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
Gle, uzvišen je Bog u svojoj snazi! Zar učitelja ima poput njega?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Tko je njemu put njegov odredio? Tko će mu reći: 'Radio si krivo'?
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Spomeni se veličati mu djelo što ga pjesmama ljudi opjevaše.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
S udivljenjem svijet čitav ga promatra, divi se čovjek, pa ma izdaleka.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
Veći je Bog no što pojmit' možemo, nedokučiv je broj ljeta njegovih!
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
U visini on skuplja kapi vode te dažd u paru i maglu pretvara.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
Pljuskovi tada pljušte iz oblaka, po mnoštvu ljudskom dažde obilato.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Tko li će shvatit' širenje oblaka, tutnjavu strašnu njegovih šatora?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
Gle, on nad sobom razastire svjetlost i dno morsko on vodama pokriva.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
Pomoću njih on podiže narode, u izobilju hranom ih dariva.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
On munju drži objema rukama i kazuje joj kamo će zgoditi.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Glasom gromovnim sebe navješćuje, stiže s gnjevom da zgromi opačinu.

< Ayuba 36 >