< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Y respondió Eliú, y dijo:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Oíd sabios, mis palabras, y doctos escuchádme:
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Porque el oído prueba las palabras, y el paladar gusta para comer.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Escojamos para vosotros el juicio, conozcamos entre nosotros cual sea lo bueno.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Porque Job ha dicho: Yo soy justo, y Dios me ha quitado mi derecho.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
En mi juicio yo fui mentiroso, mi saeta es gravada sin haber yo prevaricado.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
¿Qué hombre hay como Job, que bebe el escarnio como agua?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Y va en compañía con los que obran iniquidad, y anda con los hombres maliciosos.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Porque dijo: De nada servirá al hombre, si conformare su voluntad con Dios.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Por tanto varones de seso, oídme: Lejos vaya de Dios la impiedad, y del Omnipotente la iniquidad.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Porque él pagará al hombre su obra, y él le hará hallar conforme a su camino,
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Además de esto, cierto Dios no hará injusticia, y el Omnipotente no pervertirá el derecho.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
¿Quién visitó por él la tierra? ¿y quién puso en orden todo el mundo?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Si él pusiese sobre el hombre su corazón, y recogiese a sí su espíritu y su aliento,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
Toda carne perecería juntamente, y el hombre se tornaría en polvo.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Y si hay en ti entendimiento, oye esto: escucha la voz de mis palabras.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
¿Enseñorearse ha el que aborrece juicio? ¿y condenarás al poderoso siendo justo?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
¿Decirse ha al rey: Perverso eres; y a los príncipes: Impíos sois?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
¿ Cuánto menos a aquel que no hace acepción de personas de príncipes, ni el rico es de él más respetado que el pobre? porque todos son obras de sus manos.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
En un momento mueren, y a media noche se alborotarán los pueblos, y pasarán, y sin mano será quitado el poderoso.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Porque sus ojos están sobre los caminos del hombre, y todos sus pasos ve.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
No hay tinieblas, ni sombra de muerte, donde se encubran los que obran maldad.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Porque nunca más permitirá al hombre, que vaya con Dios a juicio.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Él quebrantará a los fuertes sin pesquisa: y hará estar otros en lugar de ellos.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Por tanto él hará notorias las obras de ellos; y volverá la noche, y serán quebrantados.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Como a malos los herirá en lugar donde sean vistos.
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Por cuanto se apartaron de él así, y no consideraron todos sus caminos:
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Haciendo venir delante de sí el clamor del pobre, y oyendo el clamor de los necesitados.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Y si él diere reposo, ¿quién inquietará? Si escondiere el rostro, ¿quién le mirará? Esto sobre una nación, y asimismo sobre un hombre:
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Haciendo que reine el hombre hipócrita para escándalos del pueblo.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Porque de Dios es decir: Yo perdoné, no destruiré.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Enséñame tú lo que yo no veo: que si hice mal, no lo haré más.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
¿ Ha de ser eso según tu mente? Él te recompensará, que no quieras tú, o quieras, y no yo: di lo que sabes.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Los hombres de seso dirán conmigo, y el hombre sabio me oirá.
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job no habla con sabiduría, y sus palabras no son con entendimiento.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Deseo que Job sea probado luengamente: para que haya respuestas contra los varones inicuos.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Por cuanto a su pecado añadió impiedad: bate las manos entre nosotros, y multiplica sus palabras contra Dios.

< Ayuba 34 >