< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Además, Eliú respondió,
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Escuchad mis palabras, sabios. Escúchame, tú que tienes conocimiento.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Porque el oído prueba las palabras, como el paladar prueba la comida.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Escojamos para nosotros lo que es correcto. Conozcamos entre nosotros lo que es bueno.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Porque Job ha dicho: “Soy justo”, Dios me ha quitado el derecho.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
A pesar de mi derecho se me considera un mentiroso. Mi herida es incurable, aunque estoy sin desobediencia’.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Qué hombre es como Job, que bebe el desprecio como el agua,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
que va en compañía de los obreros de la iniquidad, y camina con los hombres malvados?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Porque él ha dicho: “De nada le sirve al hombre para que se deleite con Dios”.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
“Por tanto, escuchadme, hombres de entendimiento: lejos de Dios, que haga la maldad, del Todopoderoso, para que cometa iniquidad.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Porque el trabajo de un hombre se lo devolverá, y haz que cada uno encuentre según sus caminos.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Sí, ciertamente, Dios no hará maldad, ni el Todopoderoso pervertirá la justicia.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
¿Quién lo puso a cargo de la tierra? ¿O quién lo ha designado sobre el mundo entero?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Si pone su corazón en sí mismo, si reuniera para sí su espíritu y su aliento,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
toda la carne perecería junta, y el hombre volvería a convertirse en polvo.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
“Si ahora tienes entendimiento, escucha esto. Escucha la voz de mis palabras.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
¿Debe gobernar incluso quien odia la justicia? ¿Condenarás al que es justo y poderoso,
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
que dice a un rey: “¡Vil! o a los nobles, “¡malvados!”?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
No respeta las personas de los príncipes, ni respetar a los ricos más que a los pobres, porque todos son obra de sus manos.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
En un momento mueren, incluso a medianoche. El pueblo se estremece y fallece. A los poderosos se les quita la mano.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
“Porque sus ojos están en los caminos del hombre. Él ve todas sus salidas.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
No hay oscuridad, ni tinieblas espesas, donde los obreros de la iniquidad pueden esconderse.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Porque no necesita considerar más a un hombre, que debe ir ante Dios en el juicio.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
El rompe en pedazos a los hombres poderosos de una manera que no se puede descubrir, y pone a otros en su lugar.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Por eso toma conocimiento de sus obras. Él los derriba en la noche, para que sean destruidos.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Los golpea como hombres malvados a la vista de los demás;
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
porque se apartaron de seguirlo, y no prestaba atención a ninguna de sus formas,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
de modo que hicieron llegar a él el clamor de los pobres. Oyó el clamor de los afligidos.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Cuando da tranquilidad, ¿quién puede entonces condenar? Cuando esconde su rostro, ¿quién puede verlo entonces? Está sobre una nación o un hombre por igual,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
para que no reine el hombre impío, para que no haya nadie que engañe al pueblo.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
“Porque ¿ha dicho alguno a Dios, ‘Soy culpable, pero no ofenderé más.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Enséñame lo que no veo. Si he hecho iniquidad, no la haré más’?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
¿Será su recompensa como deseas, que la rechaces? Porque tú debes elegir, y no yo. Por lo tanto, habla de lo que sabes.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Los hombres de entendimiento me dirán, sí, todo sabio que me escuche:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
“Job habla sin conocimiento. Sus palabras carecen de sabiduría”.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Deseo que Job sea juzgado hasta el final, a causa de su respuesta como hombres malvados.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Porque añade la rebelión a su pecado. Aplaude entre nosotros, y multiplica sus palabras contra Dios”.

< Ayuba 34 >