< Ayuba 34 >
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Escuchen mis palabras, hombres que se creen sabios; presten atención a lo que digo, ustedes que creen que saben.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
El oído distingue las palabras igual que el paladar distingue los alimentos.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Discernamos por nosotros mismos lo que es justo; decidamos entre nosotros lo que es bueno.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Job dijo: ‘Soy inocente, y Dios me ha negado la justicia.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Aunque tengo razón, me tratan como a un mentiroso; me estoy muriendo de mis heridas, aunque no he hecho nada malo’.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
“¿Ha habido alguna vez un hombre como Job con tanta sed de ridiculizar a los demás?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Se hace compañía de gente malvada; se asocia con los que hacen el mal.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Incluso ha dicho: ‘¿De qué sirve ser amigo de Dios?’
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
“¡Así que escúchenme, hombres de entendimiento! Es imposible que Dios haga el mal y que el Todopoderoso actué con maldad.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Él paga a la gente por lo que ha hecho y la trata como se merece.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Es absolutamente seguro que Dios no actúa con maldad; el Todopoderoso nunca pervertiría la justicia.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
¿Quién lo puso a cargo de la tierra? ¿Quién le dio la responsabilidad de todo el mundo?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Si se retirara su espíritu, si recuperara su aliento,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
todos los seres vivos morirían inmediatamente y los seres humanos volverían al polvo.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
“Si tienen entendimiento, escuchen esto; presten atención a lo que digo.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
¿De verdad crees que puede gobernar alguien que odia la justicia? ¿Vas a condenar a Dios Todopoderoso, que siempre hace lo que es justo?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Él es quien dice a los reyes: ‘Ustedes son unos inútiles’, o a los nobles: ‘Ustedes son unos malvados’.
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
No tiene en mayor consideración a los ricos que a los pobres, pues todos son personas que él mismo hizo.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Mueren en un momento; a medianoche se estremecen y pasan; los poderosos se van sin esfuerzo.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
“Porque él vigila lo que hacen y ve por donde van.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
No hay oscuridad tan profunda en la que los que hacen el mal puedan esconderse de él.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Dios no necesita examinar a nadie con mayor detalle para que se presente ante él para ser juzgado.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Él hace caer a los poderosos sin necesidad de una investigación; pone a otros en su lugar.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Sabiendo lo que han hecho, los derriba en una noche y los destruye.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Los derriba por su maldad en público, donde pueden ser vistos
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
porque se apartaron de seguirlo, despreciando todos sus caminos.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Hicieron que los pobres lo llamaran, y él escuchó los gritos de los oprimidos.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Pero si Dios quiere guardar silencio, ¿quién puede condenarlo? Si decide ocultar su rostro, ¿quién podrá verlo? Ya sea que se trate de una nación o de un individuo,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
una persona que rechaza a Dios no debe gobernar para no engañar a la gente.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
“Si tú le dijeras a Dios: ‘He pecado, pero ya no haré cosas malas.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Muéstrame lo que no puedo ver. Si he hecho el mal, no lo volveré a hacer’,
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
entonces, ¿debe Dios recompensarte por seguir tus propias opiniones ya que has rechazado las suyas? ¡Tú eres el que tiene que elegir, no yo! Dinos lo que piensas.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Porque la gente que entiende – los sabios que han oído lo que he dicho – me dirán
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
‘Job no sabe lo que dice. Lo que dice no tiene ningún sentido’.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Si tan solo Job fuera condenado porque habla como lo hacen los malvados.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Ahora ha añadido la rebeldía a sus pecados y nos aplaude, haciendo largos discursos llenos de acusaciones contra Dios”.