< Ayuba 34 >
Tomó de nuevo la palabra Eliú y dijo:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Oíd, oh sabios, mis palabras; hombres prudentes, prestadme oído;
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
porque el oído prueba las palabras, como el paladar los manjares.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Procuremos elegirnos lo justo, conozcamos lo bueno en medio nuestro.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Job dice: «Yo soy justo, pero Dios no quiere hacerme justicia;
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
al sostener mi derecho paso por mentiroso; incurable es mi llaga, sin que haya en mi pecado.»
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
¿Qué hombre hay semejante a Job, que se bebe las blasfemias como agua,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
que va en compañía con los obradores de iniquidad, y anda con los hombres perversos?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Pues dice: «No saca ningún provecho el que procura agradar a Dios.»
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Oídme, por tanto, hombres sensatos: ¡Lejos de Dios la maldad, lejos del Todopoderoso la injusticia!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Él da a las obras del hombre su pago, retribuye según la conducta de cada uno.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Es imposible que Dios haga maldad; no viola el Omnipotente la justicia.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
¿Quién le puso sobre la tierra? ¿Quién le ha confiado el universo?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Si Él mirase al hombre y retirara hacia sí su espíritu y su soplo,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
de golpe moriría toda carne, y el hombre volvería al polvo.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Si tienes entendimiento, escucha esto, atiende a la voz de mis palabras.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
¿Acaso puede gobernar un enemigo de la justicia? ¿Pretendes tú por ventura condenar al Justo poderoso?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
A aquel que dice a un rey: «¡Malvado!» y a los nobles: «¡Perversos!»
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
A aquel que no prefiere la persona de los grandes, ni mira al rico más que al pobre, porque todos son obra de sus manos.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
De repente mueren, en medio de la noche; pueblos enteros son sacudidos y desaparecen; son quitados los poderosos, sin fuerza (de hombre).
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Porque Sus ojos observan los caminos del hombre, y Él ve todos sus pasos.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
No hay tiniebla, no hay oscuridad tan densa, que puedan esconderse en ella los obradores de iniquidad.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Él no necesita tiempo en el examen del hombre, para llamarlo ante Dios a juicio.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Él quebranta a los poderosos sin necesidad de investigación, y pone a otros en su lugar.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Por eso, conociendo las obras de ellos los derriba de noche y están destruidos.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Los castiga, siendo como son malos, en un lugar donde (todos) lo ven,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
porque alejándose de Él, no quisieron saber nada de sus caminos.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Hicieron llegar a Él el clamor de los humildes, y Él oyó el lamento de los afligidos.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Cuando Él calla, ¿quién podrá condenarlo? si esconde su rostro, ¿quién le verá, ya sea nación o bien un particular?
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Así pone fin al dominio del impío, para que no sirva más de lazo para el pueblo.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Si ahora dice a Dios: «He soportado (tu castigo), no pecaré más;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
enséñame Tú lo que yo no veo; si he hecho iniquidad, no la haré más.»
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
¿Acaso Él debe darte el pago según el parecer tuyo, según tu negativa o conformidad? Yo no (pienso) así. Di, pues, lo que sabes.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Los hombres sensatos me dirán, lo mismo que los sabios que me oyen:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
«Job ha hablado neciamente, sus palabras fueron imprudentes.»
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
¡Ojalá sea Job probado hasta el fin, por sus respuestas de hombre impío!
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Porque a su pecado añade la rebelión, bate palmas en medio de nosotros, y habla cada vez más contra Dios.”