< Ayuba 34 >
Још говори Елијуј и рече:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Чујте, мудри, беседу моју, и разумни послушајте ме.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Јер ухо познаје беседу као што грло куша јело.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Разаберимо шта је право, извидимо међу собом шта је добро.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Јер Јов рече: Праведан сам, а Бог одбаци моју правду.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Хоћу ли лагати за своју правду? Стрела је моја смртна, а без кривице.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Који је човек као Јов да као воду пије подсмех?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
И да се дружи с онима који чине безакоње, и да ходи с безбожним људима?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Јер рече: Не помаже човеку да угађа Богу.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Зато, људи разумни, послушајте ме; далеко је од Бога злоћа и неправда од Свемогућег.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Јер по делу плаћа човеку и даје сваком да нађе према путу свом.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Доиста Бог не ради зло и Свемогући не изврће правде.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Ко Му је предао земљу? И ко је уредио васиљену?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Кад би на себе окренуо срце своје, узео би к себи дух свој и дисање своје;
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
Изгинуло би свако тело, и човек би се вратио у прах.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Ако си, дакле, разуман, чуј ово: слушај глас речи мојих.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Може ли владати онај који мрзи на правду? Хоћеш ли осудити оног који је најправеднији?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Каже ли се цару: Ниткове! И кнезовима: Безбожници?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
А камо ли Ономе који не гледа кнезовима ко су, нити у Њега вреди више богати од сиромаха, јер су сви дело руку Његових.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Умиру за час, и у по ноћи усколеба се народ и пропадне, и однесе се јаки без руке људске.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Јер су очи Његове обраћене на путеве човечије и види све кораке његове.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Нема мрака ни сена смртнога где би се сакрили који чине безакоње.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Јер никоме не одгађа кад дође да се суди с Богом.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Сатире јаке недокучиво, и поставља друге на њихово место.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Јер зна дела њихова, и док обрати ноћ, сатру се.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Као безбожне разбија их на видику.
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Јер одступише од Њега и не гледаше ни на које путеве Његове;
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Те дође до Њега вика сиромахова, и чу вику невољних.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Кад Он умири, ко ће узнемирити? И кад Он сакрије лице, ко ће Га видети? И то бива и народу и човеку.
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Да не би царовао лицемер, да не би било замке народу.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Заиста, треба казати Богу: Подносио сам, нећу више грешити.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
А шта не видим, Ти ме научи; ако сам чинио неправду, нећу више.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Еда ли ће по теби плаћати, јер теби није по вољи, јер ти бираш а не Он? Ако знаш шта, говори.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Људи ће разумни са мном казати, и мудар ће човек пристати,
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Да Јов не говори разумно, и да речи његове нису мудре.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Оче мој, нека се Јов искуша до краја, што одговара као зли људи.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Јер домеће на грех свој безакоње, пљеска рукама међу нама, и много говори на Бога.