< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
И продолжал Елиуй и сказал:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
выслушайте, мудрые, речь мою, и приклоните ко мне ухо, рассудительные!
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Ибо ухо разбирает слова, как гортань различает вкус в пище.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Установим между собою рассуждение и распознаем, что хорошо.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Вот, Иов сказал: я прав, но Бог лишил меня суда.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Должен ли я лгать на правду мою? Моя рана неисцелима без вины.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Есть ли такой человек, как Иов, который пьет глумление, как воду,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
вступает в сообщество с делающими беззаконие и ходит с людьми нечестивыми?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Потому что он сказал: нет пользы для человека в благоугождении Богу.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Итак послушайте меня, мужи мудрые! Не может быть у Бога неправда или у Вседержителя неправосудие,
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
ибо Он по делам человека поступает с ним и по путям мужа воздает ему.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Истинно, Бог не делает неправды и Вседержитель не извращает суда.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Кто кроме Его промышляет о земле? И кто управляет всею вселенною?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Если бы Он обратил сердце Свое к Себе и взял к Себе дух ее и дыхание ее, -
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
вдруг погибла бы всякая плоть, и человек возвратился бы в прах.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Итак, если ты имеешь разум, то слушай это и внимай словам моим.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Ненавидящий правду может ли владычествовать? И можешь ли ты обвинить Всеправедного?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Можно ли сказать царю: ты - нечестивец, и князьям: вы - беззаконники?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Но Он не смотрит и на лица князей и не предпочитает богатого бедному, потому что все они дело рук Его.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Внезапно они умирают; среди ночи народ возмутится, и они исчезают; и сильных изгоняют не силою.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Ибо очи Его над путями человека, и Он видит все шаги его.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Нет тьмы, ни тени смертной, где могли бы укрыться делающие беззаконие.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Потому Он же не требует от человека, чтобы шел на суд с Богом.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Он сокрушает сильных без исследования и поставляет других на их места;
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
потому что Он делает известными дела их и низлагает их ночью, и они истребляются.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Он поражает их, как беззаконных людей, пред глазами других,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
за то, что они отвратились от Него и не уразумели всех путей Его,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
так что дошел до Него вопль бедных, и Он услышал стенание угнетенных.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Дарует ли Он тишину, кто может возмутить? скрывает ли Он лице Свое, кто может увидеть Его? Будет ли это для народа, или для одного человека,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
чтобы не царствовал лицемер к соблазну народа.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
К Богу должно говорить: я потерпел, больше не буду грешить.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
А чего я не знаю, Ты научи меня; и если я сделал беззаконие, больше не буду.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
По твоему ли рассуждению Он должен воздавать? И как ты отвергаешь, то тебе следует избирать, а не мне; говори, что знаешь.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Люди разумные скажут мне, и муж мудрый, слушающий меня:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Иов не умно говорит, и слова его не со смыслом.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Я желал бы, чтобы Иов вполне был испытан, по ответам его, свойственным людям нечестивым.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Иначе он ко греху своему прибавит отступление, будет рукоплескать между нами и еще больше наговорит против Бога.

< Ayuba 34 >