< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Og Elihu tok atter til orde og sa:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Hør mine ord, I vise, og lån mig øre, I forstandige!
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Øret prøver jo ord, likesom ganen smaker mat.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
La oss velge det som er rett; la oss sammen søke å finne ut hvad der er godt!
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Job har jo sagt: Jeg er rettferdig, og Gud har tatt min rett fra mig;
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
tross min rett skal jeg være en løgner; en drepende pil har rammet mig, enda der ingen brøde er hos mig.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Hvem er en mann som Job, han som drikker bespottelse som vann
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
og gir sig i lag med dem som gjør ondt, og søker omgang med ugudelige menn?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For han har sagt: En mann har intet gagn av at han holder vennskap med Gud.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Derfor, I forstandige, hør på mig! Det være langt fra Gud å gjøre noget syndig og fra den Allmektige å være urettferdig!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Han lønner mennesket efter dets gjerninger og gjengjelder mannen efter hans ferd.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Ja sannelig, Gud gjør ikke noget syndig, og den Allmektige forvender ikke retten.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Hvem har overgitt jorden til hans varetekt, og hvem har overlatt hele jorderike til ham?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Dersom han bare vilde tenke på sig selv og dra sin Ånd og sin ånde til sig igjen,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
da skulde alt kjød opgi ånden på én gang, og mennesket bli til støv igjen.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Men gi nu akt og hør på dette, lytt nøye til mine ord!
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Kan vel en som hater retten, være hersker? Eller tør du fordømme den Rettferdige, den Mektige?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Sier vel nogen til en konge: Din niding, eller til en fyrste: Du ugudelige?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Gud tar jo ikke parti for fyrster og akter ikke en rik høiere enn en fattig? De er jo alle hans henders verk.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
I et øieblikk dør de, midt om natten; folket raver og forgår, og den mektige rykkes bort, ikke ved menneskehånd.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For hans øine vokter på hver manns veier, og han ser alle hans skritt;
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
det finnes intet mørke og ingen dødsskygge hvor de som gjør ondt kan skjule sig;
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Gud har ikke nødig å gi lenge akt på en mann før han må møte for Guds dom.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Han knuser de mektige uten å granske deres sak og setter så andre i deres sted.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Ja, han kjenner deres gjerninger, og han slår dem ned om natten så de går til grunne.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Han tukter dem som ugjerningsmenn, på et sted hvor alle kan se det;
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
for derfor vek de bort fra ham og aktet ikke på nogen av hans veier,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
forat de skulde la de fattiges skrik komme for ham, forat han skulde høre de undertryktes rop.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Lar han være å skride inn, hvem tør da fordømme ham? Skjuler han sitt åsyn, hvem får da se ham? Både med et folk og med et enkelt menneske gjør han jo således,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
forat et gudløst menneske ikke skal herske, forat det ikke skal være snarer for folket.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
For har vel et slikt menneske nogensinne sagt til Gud: Jeg har vært overmodig, jeg vil herefter ikke gjøre det som ondt er;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
det jeg ikke ser, det må du lære mig; har jeg gjort urett, så vil jeg ikke gjøre det mere?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Skulde han vel gjengjelde efter ditt tykke? Du har jo klandret ham. Så må du velge og ikke jeg, og hvad du vet, får du si.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Forstandige menn vil si til mig, ja hver vismann som hører på mig:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job taler uten skjønnsomhet, og hans ord er ikke forstandige.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Gid Job måtte bli prøvd uavlatelig, fordi han har svart på onde menneskers vis!
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
For til sin synd legger han brøde; her iblandt oss klapper han i hendene og bruker mange ord om Gud.

< Ayuba 34 >