< Ayuba 34 >
U-Elihu waqhubeka esithi:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Zwanini amazwi ami, lina madoda ahlakaniphileyo; lalelani kimi, lina madoda ayizifundiswa.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Phela indlebe iyawahlola amazwi njengolimi lunambitha ukudla.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Asizihluzeleni thina okulungileyo; kasifundeni ndawonye okuhle.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
UJobe uthi, ‘Kangilacala, kodwa uNkulunkulu kangahluleli ngokulunga.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Loba mina ngiqondile, kuthiwa ngilamanga; loba ngingelacala, umtshoko wakhe ungihlaba isilonda esingelaphekiyo.’
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
UJobe kanti ungumuntu bani, onatha ukuklolodela njengamanzi?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Uzwanana labantu abenza ububi; uhambisana labantu ababi.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Ngoba uthi, ‘Umuntu kakumsizi ngalutho ukuzama ukuthokozisa uNkulunkulu.’
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Ngakho lalelani kimi lina madoda azwisisayo. Kakube khatshana laye uNkulunkulu ukwenza ububi, khatshana kukaSomandla ukona.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Uyamphindisela umuntu ngalokho akwenzileyo; umehlisela lokho okufanele ukuziphatha kwakhe.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Kakungeni engqondweni ukuthi uNkulunkulu angenza ububi, ukuthi uSomandla angakutshila ukwahlulela ngokulunga.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Ngubani owambekayo phezu komhlaba na? Ngubani owathi kalawule umhlaba wonke na?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Aluba wayengathanda asuse umoya wakhe lokuphefumula,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
bonke abantu babengatshabalala kanyekanye, umuntu wayezabuyela othulini.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Nxa lilokuzwisisa, zwanini lokhu; lalelani lokhu engikutshoyo.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Kambe lowo ozonda ukwahlulela ngokulunga angabusa na? Liyamlahla yini Yena oqotho njalo olamandla?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Kayisuye yini othi emakhosini, ‘Kalisizi lutho,’ athi kwabayizikhulu, ‘Libabi,’
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
ongatshengisi ukwazisa amakhosana kulabanye loba athande abanothileyo kulabayanga, ngoba bonke bangumsebenzi wezandla zakhe?
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Bayafa nje masinyane, loba phakathi kobusuku; abantu bayanyikinywa bedlule; abalamandla bayasuswa kungelasandla somuntu.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Amehlo akhe aphezu kwezindlela zabantu; ubona zonke izinyathelo zabo.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Akulandawo emnyama loba ithunzi elisithileyo, lapho abenzi bobubi abangacatsha khona.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
UNkulunkulu kasweli ukuthi aphinde abahlolisise abantu, ukuze abalethe ekwahlulelweni phambi kwakhe.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Engaqalanga wahlola uyabaphahlaza abalamandla abeke abanye endaweni yabo.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Ngoba ezinanzelela izenzo zabo, uyabagenqula ebusuku bahlifizeke.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Uyabajezisa ngenxa yobubi babo kube segcekeni emuntwini wonke,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
ngoba baphambuka ekumlandeleni abaze banaka layiphi indlela yakhe.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Benza ukukhala kwabayanga kweza phambi kwakhe, laye wakuzwa ukukhala kwabasweleyo.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Kodwa nxa elokhu ezithulele, ngubani ongamsola na? Angafihla ubuso bakhe ngubani ongambona na? Kanti uphezu komuntu lesizwe ngokufanayo,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
ukwalela ongamesabiyo uNkulunkulu ukuthi abuse, ukuze angafakeli abantu izifu.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Akesithi umuntu athi kuNkulunkulu, ‘Ngilecala kodwa kangisayikona njalo.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Ngifundisa lokho engingakuboniyo; nxa ngenze okubi, kangisayikuphinda ngikwenze.’
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Pho uNkulunkulu akuvuze ngokwentando yakho na, wena usala ukuphenduka? Kumele ukhethe wena, hatshi mina; ngakho ngitshela lokho okwaziyo.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Amadoda alokuqedisisa azakutsho, amadoda ahlakaniphileyo abangizwayo ngisithi kini,
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
‘UJobe ukhuluma engelalwazi; amazwi akhe kawalambono.’
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Oh, uJobe angasake alingwe ngokweqileyo ngoba uphendule njengomuntu omubi!
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Phezu kwesono sakhe wengeza ukuhlamuka; uyakloloda ngokuqakeza izandla zakhe phakathi kwethu andise amazwi akhe aphikisa uNkulunkulu.”