< Ayuba 34 >
Und es hob an Elihu und sprach:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Hört, ihr Weisen, meine Rede, und ihr Verständigen, merkt auf mich!
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Denn das Ohr prüft die Rede, und der Mund schmeckt die Speise.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Laßt uns ein Urteil finden, daß wir erkennen unter uns, was gut sei.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Denn Hiob hat gesagt: “Ich bin gerecht, und Gott weigert mir mein Recht;
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
ich muß lügen, ob ich wohl recht habe, und bin gequält von meinen Pfeilen, ob ich wohl nichts verschuldet habe.”
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Wer ist ein solcher Hiob, der da Spötterei trinkt wie Wasser
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
und auf dem Wege geht mit den Übeltätern und wandelt mit gottlosen Leuten?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Denn er hat gesagt: “Wenn jemand schon fromm ist, so gilt er doch nichts bei Gott.”
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Darum hört mir zu, ihr weisen Leute: Es sei ferne, daß Gott sollte gottlos handeln und der Allmächtige ungerecht;
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
sondern er vergilt dem Menschen, darnach er verdient hat, und trifft einen jeglichen nach seinem Tun.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Ohne zweifel, Gott verdammt niemand mit Unrecht, und der Allmächtige beugt das Recht nicht.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Wer hat, was auf Erden ist, verordnet, und wer hat den ganzen Erdboden gesetzt?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
So er nun an sich dächte, seinen Geist und Odem an sich zöge,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
so würde alles Fleisch miteinander vergehen, und der Mensch würde wieder zu Staub werden.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Hast du nun Verstand, so höre das und merke auf die Stimme meiner Reden.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Kann auch, der das Recht haßt regieren? Oder willst du den, der gerecht und mächtig ist, verdammen?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Sollte einer zum König sagen: “Du heilloser Mann!” und zu den Fürsten: “Ihr Gottlosen!”?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Und er sieht nicht an die Person der Fürsten und kennt den Herrlichen nicht mehr als den Armen; denn sie sind alle seiner Hände Werk.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Plötzlich müssen die Leute sterben und zu Mitternacht erschrecken und vergehen; die Mächtigen werden weggenommen nicht durch Menschenhand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Denn seine Augen sehen auf eines jeglichen Wege, und er schaut alle ihre Gänge.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Es ist keine Finsternis noch Dunkel, daß sich da möchten verbergen die Übeltäter.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Denn er darf auf den Menschen nicht erst lange achten, daß er vor Gott ins Gericht komme.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Er bringt die Stolzen um, ohne erst zu forschen, und stellt andere an ihre Statt:
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
darum daß er kennt ihre Werke und kehrt sie um des Nachts, daß sie zerschlagen werden.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Er straft sie ab wie die Gottlosen an einem Ort, da man es sieht:
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
darum daß sie von ihm weggewichen sind und verstanden seiner Wege keinen,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
daß das Schreien der Armen mußte vor ihn kommen und er das Schreien der Elenden hörte.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Wenn er Frieden gibt, wer will verdammen? und wenn er das Antlitz verbirgt, wer will ihn schauen unter den Völkern und Leuten allzumal?
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Denn er läßt nicht über sie regieren einen Heuchler, das Volk zu drängen.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Denn zu Gott muß man sagen: “Ich habe gebüßt, ich will nicht übel tun.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Habe ich's nicht getroffen, so lehre du mich's besser; habe ich Unrecht gehandelt, ich will's nicht mehr tun.”
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Soll er nach deinem Sinn vergelten? Denn du verwirfst alles; du hast zu wählen, und nicht ich. Weißt du nun was, so sage an.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Verständige Leute werden zu mir sagen und ein weiser Mann, der mir zuhört:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
“Hiob redet mit Unverstand, und seine Worte sind nicht klug.”
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
O, daß Hiob versucht würde bis ans Ende! darum daß er sich zu ungerechten Leuten kehrt.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Denn er hat über seine Sünde noch gelästert; er treibt Spott unter uns und macht seiner Reden viel wider Gott.