< Ayuba 34 >
Und Elihu hob wieder an und sprach:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Höret, ihr Weisen, meine Worte, und ihr Kundigen, gebet mir Gehör!
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Denn das Ohr prüft die Worte, wie der Gaumen die Speise kostet. [Eig. speisend kostet]
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Erwählen wir für uns, was recht, erkennen wir unter uns, was gut ist!
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Denn Hiob hat gesagt: Ich bin gerecht, und Gott [El] hat mir mein Recht entzogen.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Trotz meines Rechtes soll ich lügen; meine Wunde [Eig. mein Pfeil; vergl. Kap. 6,4;16,13] ist unheilbar, ohne daß ich übertreten habe. -
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Wer ist ein Mann wie Hiob, der Hohn trinkt wie Wasser,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
und in Gesellschaft geht mit denen, die Frevel tun, und wandelt mit gottlosen Menschen?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Denn er hat gesagt: Keinen Nutzen hat ein Mann davon, daß er Wohlgefallen an Gott hat! [Eig. gern mit Gott verkehrt]
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Darum höret mir zu, ihr Männer von Verstand! Fern sei Gott von Gesetzlosigkeit, und der Allmächtige von Unrecht!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Sondern des Menschen Tun vergilt er ihm, und nach jemandes Wege läßt er es ihn finden.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Ja, wahrlich, Gott [El] handelt nicht gesetzlos, und der Allmächtige beugt nicht das Recht.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Wer hat ihm die Erde anvertraut? Und wer den ganzen Erdkreis gegründet? [Eig. gesetzt]
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Wenn er sein Herz nur auf sich selbst richtete, seinen Geist [O. Hauch] und seinen Odem an sich zurückzöge,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
so würde alles Fleisch insgesamt verscheiden, und der Mensch zum Staube zurückkehren.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Und wenn du doch dieses einsehen und hören, der Stimme meiner Worte Gehör schenken wolltest!
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Sollte auch herrschen, wer das Recht haßt? oder willst du den Allgerechten [W. den Gerecht-Mächtigen] verdammen?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Sagt man zu einem Könige: Belial, [Nichtswürdiger] zu Edlen: Du Gottloser? -
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Wieviel weniger zu ihm, der die Person der Fürsten nicht ansieht und den Reichen [O. Vornehmen] nicht vor dem Armen berücksichtigt! Denn sie alle sind das Werk seiner Hände.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
In einem Augenblick sterben sie; und in der Mitte der Nacht wird ein Volk erschüttert und vergeht, und Mächtige werden beseitigt ohne Hand. [Eig. nicht durch Hand [d. h. Menschenhand]]
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Denn seine Augen sind auf die Wege des Menschen gerichtet, und er sieht alle seine Schritte.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Da ist keine Finsternis und kein Todesschatten, daß sich darein verbergen könnten, die Frevel tun.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Denn er braucht nicht lange auf einen Menschen acht zu geben, damit er vor Gott [El] ins Gericht komme.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Er zerschmettert Gewaltige ohne Untersuchung, und setzt andere an ihre Stelle.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Daher kennt er ihre Handlungen, und kehrt sie um über Nacht; und sie werden zermalmt.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Er schlägt sie, wie Übeltäter, auf öffentlichem Platze,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
darum daß sie von seiner Nachfolge [Eig. von hinter ihm] abgewichen sind [And. üb.: denn darum sind sie usw.] und alle seine Wege nicht bedacht haben,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
um zu ihm hinaufdringen zu lassen das Schreien des Armen, und damit er das Schreien der Elenden höre.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Schafft er Ruhe, wer will beunruhigen? Und verbirgt er das Angesicht, wer kann ihn schauen? So handelt er sowohl gegen ein Volk, als auch gegen einen Menschen zumal,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
damit der ruchlose Mensch nicht regiere, damit sie nicht Fallstricke des Volkes seien.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Denn hat er wohl zu Gott [El] gesagt: Ich trage meine Strafe, ich will nicht mehr verderbt handeln;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
was ich nicht sehe, zeige du mir; wenn ich Unrecht verübt habe, so will ich es nicht mehr tun? -
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Soll nach deinem Sinne er es vergelten? Denn du hast seine Vergeltung verworfen, und so mußt du wählen, [W. denn du hast verworfen, denn du mußt wählen] und nicht ich; was du weißt, reden denn!
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Männer von Verstand werden zu mir sagen, und ein weiser Mann, der mir zuhört:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Hiob redet nicht mit Erkenntnis, und seine Worte sind ohne Einsicht.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Ach, daß doch Hiob fort und fort geprüft würde wegen seiner Antworten nach Frevlerart!
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Denn er fügt seiner Sünde Übertretung [O. Vermessenheit] hinzu, klatscht unter uns in die Hände und mehrt seine Worte gegen Gott. [El]