< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Then Elihu continued:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“You [three] men who [think that you] [SAR] are very wise, hear me; listen to what I am saying, you men who [say that you] know so much.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
When we [SYN] hear what other people [like you] say, we [RHQ] think carefully about what they say [to determine what is good and what is bad], like we [SYN] taste food [to determine what is good].
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
We need to decide [who is saying] what is right and to determine among ourselves what is good/best.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Job has said, ‘I am innocent, but God has refused to judge me fairly/justly.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Even though I have always done what is right, he is lying about me. Even though I have not done what is wrong, he has caused me to suffer, and I will certainly die.’
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
(Is there any person like Job, who insults others as easily as people accept a drink of water?/There is no person like Job, who insults others as easily as people accept a drink of water.) [RHQ]
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
He habitually associates with people who do what is evil and spends time with wicked people.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
He has said, ‘It is useless for people to try to please God.’
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
“So, you men who [claim that you] understand everything, listen to me! Almighty God would never consider doing anything that is wicked or wrong [DOU]!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
He (pays back/punishes) people for what they have done; he gives them what they deserve for the way that they have conducted their lives.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Truly, Almighty God never does what is wicked; he always [LIT] does what is fair/just.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
The authority that he has to rule everything on the earth, no one [RHQ] gave it to him; no one [RHQ] put him in control of the whole world. [He has always had that authority].
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If he would take his spirit back to himself,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
everyone would die [immediately], and their corpses would soon become dirt again.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
“So, [Job], if [you say that you] understand everything, listen to what I am saying.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
God could certainly not [RHQ] govern the world if he hated doing what is fair/just. So, will you condemn God, who is righteous and powerful, [saying that what he has done is wrong]?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
He tells [some] kings that they are worthless, and he says to [some] officials that they are wicked.
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
He does not favor rulers [more than he favors others]; he does not favor rich people more than poor people, because he created all of them.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
People [often] die suddenly; he strikes them at midnight and they die; he even gets rid of mighty people without the help of any humans [SYN].
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
“He sees [MTY] everything that people do; [when we walk, ] he watches every step that we take.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no gloom or darkness [DOU] that is so dark that sinners can hide [from him] in that darkness.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
God does not [need to] set a time when we will stand in front of him in order that he may judge us. [He can judge us whenever he wants to].
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He destroys mighty people without [needing to] investigate [what they have done], and he appoints others to take their places.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Because he [already] knows what they have done, he removes them at night and gets rid of them.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Where [many] people can see it, he strikes/punishes them because of the wicked things that they have done;
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
he strikes them because they turned away from doing what he wanted them to do and did not pay attention to any of his commands.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
They [mistreated] the poor people, with the result that those poor people cried out to God [for help], and he heard those afflicted people when they cried out [to him].
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
But if God decides to do nothing [to punish wicked people], no one can criticize/condemn him. If a godless/wicked man rules a nation, a man who tricks/deceives the people,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
and if [God] hides his face [with the result that he does not see that ruler or punish him], no one will be able to prevent that ruler [from doing those things].
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
“Job, have you or anyone else ever said to God, ‘I have been punished [for my sins], and I will not sin any more;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
so teach/show me what [sins I have committed]; if I have done anything that is evil, I will not do it any more’?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
[Job, ] you object to what God has done to you, but do you think that he will do what you want him to do? It is you who must choose [what you say to God], not I; so tell me what you are thinking about this.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
“People who have good sense, those who are wise and who listen to what I say, will say to me,
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
‘Job is speaking ignorantly; what he says is nonsense.’
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
I think that Job should be taken to a court and (put on trial/judged), because he answers [us his friends] like wicked men would answer.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
To add to the [other] sins that he has committed, he is rebelling [against God]; he shows us that he does not respect God [IDM], making long speeches [saying that God has punished him unjustly].”

< Ayuba 34 >