< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
And Elihu answers and says:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Hear, O wise men, my words, And, O knowing ones, give ear to me.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
For the ear tries words, And the palate tastes to eat.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Let us choose judgment for ourselves, Let us know among ourselves what [is] good.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
For Job has said, I have been righteous, And God has turned aside my right,
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Against my right do I lie? My arrow [is] mortal—without transgression.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Who [is] a man like Job? He drinks scoffing like water,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
And he has traveled for company With workers of iniquity, So as to go with men of wickedness.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For he has said, It does not profit a man When he delights himself with God.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Therefore, O men of heart, listen to me; Far be it from God to do wickedness, And [from] the Mighty to do perverseness,
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
For He repays the work of man to him, And according to the path of each He causes him to find.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Indeed, truly, God does not do wickedly, And the Mighty does not pervert judgment.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Who has inspected for Himself the earth? And who has placed all the habitable world?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If He sets His heart on him, [If] He gathers His Spirit and His breath to Himself,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
All flesh expires together, And man returns to dust.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
And if [there is] understanding, hear this, Give ear to the voice of my words.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Indeed, does one hating justice govern? Or do you condemn the Most Just?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Who has said to a king, Worthless, To princes, Wicked?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
That has not accepted the person of princes, Nor has known the rich before the poor, For all of them [are] a work of His hands.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
[In] a moment they die, And at midnight people shake, And they pass away, And they remove the mighty without hand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For His eyes [are] on the ways of each, And He sees all his steps.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no darkness nor death-shade, For workers of iniquity to be hidden there;
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
For He does not permit man anymore, To go to God in judgment,
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He breaks the mighty—no searching! And He appoints others in their stead.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Therefore He knows their works, And He has overturned by night, And they are bruised.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
As wicked He has struck them, In the place of beholders.
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Because that against right They have turned aside from after Him, And have considered none of His ways,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
To cause to come to Him The cry of the poor, And He hears the cry of the afflicted.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
And He gives rest, and who makes wrong? And hides the face, and who beholds it? And in reference to a nation and to a man, [It is] the same.
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
From the reigning of a profane man, From the snares of a people;
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
For has any said to God: I have taken away, I do not do corruptly,
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Besides [that which] I see, You show me, If I have done iniquity—I do not add?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Does He repay by you, that you have refused—That you choose, and not I? And what you have known, speak.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Let men of heart say to me, And a wise man is listening to me:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job—he does not speak with knowledge, And his words [are] not with wisdom.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
My Father! Let Job be tried—to victory, Because of answers for men of iniquity,
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
For he adds to his sin, He vomits transgression among us, And multiplies his sayings to God.”

< Ayuba 34 >