< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Furthermore Elihu answered and said,
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Hear my words, O you wise men; and give ear to me, you that have knowledge.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
For the ear tries words, as the mouth tastes meat.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Let us choose to us judgment: let us know among ourselves what is good.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
For Job has said, I am righteous: and God has taken away my judgment.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Should I lie against my right? my wound is incurable without transgression.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
What man is like Job, who drinks up scorning like water?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Which goes in company with the workers of iniquity, and walks with wicked men.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For he has said, It profits a man nothing that he should delight himself with God.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Therefore listen to me you men of understanding: far be it from God, that he should do wickedness; and from the Almighty, that he should commit iniquity.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
For the work of a man shall he render to him, and cause every man to find according to his ways.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Yes, surely God will not do wickedly, neither will the Almighty pervert judgment.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Who has given him a charge over the earth? or who has disposed the whole world?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If he set his heart on man, if he gather to himself his spirit and his breath;
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
All flesh shall perish together, and man shall turn again to dust.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
If now you have understanding, hear this: listen to the voice of my words.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Shall even he that hates right govern? and will you condemn him that is most just?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Is it fit to say to a king, You are wicked? and to princes, You are ungodly?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
How much less to him that accepts not the persons of princes, nor regards the rich more than the poor? for they all are the work of his hands.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
In a moment shall they die, and the people shall be troubled at midnight, and pass away: and the mighty shall be taken away without hand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For his eyes are on the ways of man, and he sees all his goings.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no darkness, nor shadow of death, where the workers of iniquity may hide themselves.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
For he will not lay on man more than right; that he should enter into judgment with God.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He shall break in pieces mighty men without number, and set others in their stead.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Therefore he knows their works, and he overturns them in the night, so that they are destroyed.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
He strikes them as wicked men in the open sight of others;
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Because they turned back from him, and would not consider any of his ways:
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
So that they cause the cry of the poor to come to him, and he hears the cry of the afflicted.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
When he gives quietness, who then can make trouble? and when he hides his face, who then can behold him? whether it be done against a nation, or against a man only:
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
That the hypocrite reign not, lest the people be ensnared.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Surely it is meet to be said to God, I have borne chastisement, I will not offend any more:
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
That which I see not teach you me: if I have done iniquity, I will do no more.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Should it be according to your mind? he will recompense it, whether you refuse, or whether you choose; and not I: therefore speak what you know.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Let men of understanding tell me, and let a wise man listen to me.
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job has spoken without knowledge, and his words were without wisdom.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
My desire is that Job may be tried to the end because of his answers for wicked men.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
For he adds rebellion to his sin, he claps his hands among us, and multiplies his words against God.

< Ayuba 34 >