< Ayuba 34 >
And Eliu continued his discourse, and said:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Hear ye, wise men, my words, and ye learned, hearken to me:
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
For the ear trieth words, and the mouth discerneth meats by the taste.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Let us choose to us judgment, and let us see among ourselves what is the best.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
For Job hath said: I am just, and God hath overthrown my judgment.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
For in judging me there is a lie: my arrow is violent without any sin.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
What man is there like Job, who drinketh up scorning like water?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Who goeth in company with them that work iniquity, and walketh with wicked men?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For he hath said: Man shall not please God, although he run with him.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Therefore, ye men of understanding, hear me: far from god be wickedness, and iniquity from the Almighty.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
For he will render to a man his work, and according to the ways of every one he will reward them.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
For in very deed God will not condemn without cause, neither will the Almighty pervert judgment.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
What other hath he appointed over the earth? or whom hath he set over the world which he made?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If he turn his heart to him, he shall draw his spirit and breath unto himself.
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
All flesh shall perish together, and man shall return into ashes.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
If then thou hast understanding, hear what is said, and hearken to the voice of my words.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Can he be healed that loveth not judgment? and how dost thou so far condemn him that is just?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Who saith to the king: Thou art an apostate: who calleth rulers ungodly?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Who accepteth not the persons of princes: nor hath regarded the tyrant, when he contended against the poor man: for all are the work of his hands.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
They shall suddenly die, and the people shall be troubled at midnight, and they shall pass, and take away the violent without hand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For his eyes are upon the ways of men, and he considereth all their steps.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no darkness, and there is no shadow of death, where they may be hid who work iniquity.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
For it is no longer in the power of man to enter into judgment with God.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He shall break in pieces many and innumerable, and shall make others to stand in their stead.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
For he knoweth their works: and therefore he shall bring night on them, and they shall be destroyed.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
He hath struck them, as being wicked, in open sight.
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Who as it were on purpose have revolted from him, and would not understand all his ways:
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
So that they caused the cry of the needy to come to him, and he heard the voice of the poor.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
For when he granteth peace, who is there that can condemn? When he hideth his countenance, who is there that can behold him, whether it regard nations, or all men?
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Who maketh a man that is a hypocrite to reign for the sins of the people?
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Seeing then I have spoken of God, I will not hinder thee in thy turn.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
If I have erred, teach thou me: if I have spoken iniquity, I will add no more.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Doth God require it of thee, because it hath displeased thee? for thou begannest to speak, and not I: but if thou know any thing better, speak.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Let men of understanding speak to me, and let a wise man hearken to me.
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
But Job hath spoken foolishly, and his words sound not discipline.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
My father, let Job be tried even to the end: cease not from the man of iniquity.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Because he addeth blasphemy upon his sins, let him be tied fast in the mean time amongst us: and then let him provoke God to judgment with his speeches.