< Ayuba 34 >
Moreover Elihu answered and said,
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Hear my words, ye wise [men]; and give ear unto me, ye that have knowledge.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
For the ear trieth words, as the palate tasteth food.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Let us choose for ourselves what is right; let us know among ourselves what is good!
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
For Job hath said, I am righteous, and God hath taken away my judgment:
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Should I lie against my right? My wound is incurable without transgression.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
What man is like Job? he drinketh up scorning like water,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
And goeth in company with workers of iniquity, and walketh with wicked men.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For he hath said, It profiteth not a man if he delight himself in God.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Therefore hearken unto me, ye men of understanding: Far be wickedness from God, and wrong from the Almighty!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
For a man's work will he render to him, and cause every one to find according to [his] way.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Yea, surely, God acteth not wickedly, and the Almighty perverteth not judgment.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Who hath entrusted to him the earth? and who hath disposed the whole world?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If he only thought of himself, [and] gathered unto him his spirit and his breath,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
All flesh would expire together, and man would return to the dust.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
If now [thou hast] understanding, hear this: give ear to the voice of my words!
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Should he that hateth right indeed govern? and wilt thou condemn the All-just?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Shall one say to a king, Belial? to nobles, Wicked?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
[How then to him] that accepteth not the persons of princes, nor regardeth the rich man more than the poor? for they are all the work of his hands.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
In a moment they die, even at midnight the people are convulsed and pass away; and the strong are taken away without hand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For his eyes are upon the ways of man, and he seeth all his steps.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no darkness, nor shadow of death, where the workers of iniquity may hide themselves.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
For he doth not long consider a man, to bring him before God in judgment.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He breaketh in pieces mighty men without inquiry, and setteth others in their stead;
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Since he knoweth their actions; and he overthroweth [them] in the night, and they are crushed.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
He striketh them as wicked men in the open sight of others,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Because they have turned back from him, and would consider none of his ways;
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
So that they cause the cry of the poor to come unto him, and he heareth the cry of the afflicted.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
When he giveth quietness, who then will disturb? and when he hideth [his] face, who shall behold him? and this towards a nation, or towards a man alike;
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
That the ungodly man reign not, that the people be not ensnared.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
For hath he said unto God, I bear [chastisement], I will not offend;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
What I see not, teach thou me; if I have done wrong, I will do so no more?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Shall he recompense according to thy mind? for thou hast refused [his judgment]; for thou so choosest, and not I; speak then what thou knowest.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Men of understanding will say to me, and a wise man who heareth me:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job hath spoken without knowledge, and his words were not with intelligence.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Would that Job may be tried unto the end, because of [his] answers after the manner of evil men!
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
For he addeth rebellion unto his sin, he clappeth [his hands] among us, and multiplieth his words against God.