< Ayuba 34 >
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“Hear my words, O wise men; give ear to me, O men of learning.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
For the ear tests words as the mouth tastes food.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Let us choose for ourselves what is right; let us learn together what is good.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
For Job has declared, ‘I am righteous, yet God has deprived me of justice.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Would I lie about my case? My wound is incurable, though I am without transgression.’
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
What man is like Job, who drinks up derision like water?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
He keeps company with evildoers and walks with wicked men.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
For he has said, ‘It profits a man nothing that he should delight in God.’
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Therefore listen to me, O men of understanding. Far be it from God to do wrong, and from the Almighty to act unjustly.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
For according to a man’s deeds He repays him; according to a man’s ways He brings consequences.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Indeed, it is true that God does not act wickedly, and the Almighty does not pervert justice.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Who gave Him charge over the earth? Who appointed Him over the whole world?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
If He were to set His heart to it and withdraw His Spirit and breath,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
all flesh would perish together and mankind would return to the dust.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
If you have understanding, hear this; listen to my words.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Could one who hates justice govern? Will you condemn the just and mighty One,
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
who says to kings, ‘You are worthless!’ and to nobles, ‘You are wicked,’
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
who is not partial to princes and does not favor rich over poor? For they are all the work of His hands.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
They die in an instant, in the middle of the night. The people convulse and pass away; the mighty are removed without human hand.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
For His eyes are on the ways of a man, and He sees his every step.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
There is no darkness or deep shadow where the workers of iniquity can hide.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
For God need not examine a man further or have him approach for judgment.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
He shatters the mighty without inquiry and sets up others in their place.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Therefore, He recognizes their deeds; He overthrows them in the night and they are crushed.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
He strikes them for their wickedness in full view,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
because they turned aside from Him and had no regard for any of His ways.
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
They caused the cry of the poor to come before Him, and He heard the outcry of the afflicted.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
But when He remains silent, who can condemn Him? When He hides His face, who can see Him? Yet He watches over both man and nation,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
that godless men should not rule or lay snares for the people.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Suppose someone says to God, ‘I have endured my punishment; I will offend no more.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Teach me what I cannot see; if I have done wrong, I will not do it again.’
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Should God repay you on your own terms when you have disavowed His? You must choose, not I; so tell me what you know.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Men of understanding will declare to me, and the wise men who hear me will say:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
‘Job speaks without knowledge; his words lack insight.’
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
If only Job were tried to the utmost for answering like a wicked man.
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
For he adds rebellion to his sin; he claps his hands among us and multiplies his words against God.”