< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Ještě mluvil Elihu, a řekl:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Poslouchejte, moudří, řečí mých, a rozumní, ušima pozorujte.
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Nebo ucho řečí zkušuje, tak jako dásně okoušejí pokrmu.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Soud sobě zvolme, a vyhledejme mezi sebou, co by bylo dobrého.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Nebo řekl Job: Spravedliv jsem, a Bůh silný zavrhl při mou.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Své-liž bych pře ukrývati měl? Přeplněna jest bolestí rána má bez provinění.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Který muž jest podobný Jobovi, ješto by pil posměch jako vodu?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
A že by všel v tovaryšství s činiteli nepravosti, a chodil by s lidmi nešlechetnými?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Nebo řekl: Neprospívá to člověku líbiti se Bohu.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
A protož, muži rozumní, poslouchejte mne. Odstup od Boha silného nešlechetnost a od Všemohoucího nepravost.
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Nebo on podlé skutků člověka odplací, a podlé toho, jaká jest čí cesta, působí, aby to nalézal.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
A naprosto Bůh silný nečiní nic nešlechetně, a Všemohoucí nepřevrací soudu.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Kdo svěřil jemu zemi? A kdo zpořádal všecken okršlek?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Kdyby se na něj obrátil, a ducha jeho i duši jeho k sobě vzal,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
Umřelo by všeliké tělo pojednou, a tak by člověk do prachu se navrátil.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Máš-li tedy rozum, poslyš toho, pusť v uši své hlas řečí mých.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Ješto ten, kterýž by v nenávisti měl soud, zdaliž by panovati mohl? Èili toho, jenž jest svrchovaně spravedlivý, za nešlechetného vyhlásíš?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Zdaliž sluší králi říci: Ó nešlechetný, a šlechticům: Ó bezbožní?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Mnohem méně tomu, kterýž nepřijímá osob knížat, aniž u něho má přednost urozený před nuzným; nebo dílo rukou jeho jsou všickni.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
V okamžení umírají, třebas o půl noci postrčeni bývají lidé, a pomíjejí, a zachvácen bývá silný ne rukou lidskou.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Nebo oči jeho hledí na cesty člověka, a všecky kroky jeho on spatřuje.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Neníť žádných temností, ani stínu smrti, kdež by se skryli činitelé nepravosti.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Aniž zajisté vzkládá na koho více, tak aby se s Bohem silným souditi mohl.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Pyšné stírá bez počtu, a postavuje jiné na místa jejich.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
Nebo zná skutky jejich; pročež na ně obrací noc, a potříni bývají.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Jakožto bezbožné rozráží je na místě patrném,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Proto že odstoupili od něho, a žádných cest jeho nešetřili,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Aby dokázal, že připouští k sobě křik nuzného, a volání chudých že vyslýchá.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
(Nebo když on spokojí, kdo znepokojí? A když skryje tvář svou, kdo jej spatří?) Tak celý národ, jako i každého člověka jednostejně,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Aby nekraloval člověk pokrytý, aby nebylo lidem ourazu.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Jistě žeť k Bohu silnému raději toto mluveno býti má: Ponesuť, nezruším.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Mimo to, nevidím-li čeho, ty vyuč mne; jestliže jsem nepravost páchal, neučiním toho víc.
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Nebo zdali vedlé tvého zdání odplacovati má, že bys ty toho neliboval, že bys ono zvoloval, a ne on? Pakli co víš jiného, mluv.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Muži rozumní se mnou řeknou, i každý moudrý poslouchaje mne,
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Že Job hloupě mluví, a slova jeho nejsou rozumná.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Ó by zkušen byl Job dokonale, pro odmlouvání nám jako lidem nepravým,
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Poněvadž k hříchu svému přidává i nešlechetnost, mezi námi také jen chloubu svou vynáší, a rozmnožuje řeči své proti Bohu.

< Ayuba 34 >