< Ayuba 34 >
Elihu nastavi svoju besjedu i reče:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
“I vi, mudraci, čujte što ću reći, vi, ljudi umni, poslušajte mene,
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
jer uši nam prosuđuju besjede isto kao što nepce hranu kuša.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Zajedno ispitajmo što je pravo i razmislimo skupa što je dobro.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Job je utvrdio: 'Ja sam pravedan, ali Bog meni pravdu uskraćuje.
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
U pravu sam, a lašcem prave mene, nasmrt prostrijeljen, a bez krivnje svoje!'
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Zar gdje čovjeka ima poput Joba koji porugu pije kao vodu,
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
sa zlikovcima koji skupa hodi i s opakima isti dijeli put?
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
On tvrdi: 'Kakva korist je čovjeku od tog što Bogu ugoditi želi?'
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
Stoga me čujte, vi ljudi pametni! Od Boga zlo je veoma daleko i nepravednost od Svemogućega,
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
te on čovjeku plaća po djelima, daje svakom po njegovu vladanju.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Odista, Bog zla nikada ne čini, niti Svesilni kad izvrće pravo.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
TÓa tko je njemu povjerio zemlju i vasioni svijet tko je stvorio?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
Kad bi on dah svoj u se povukao, kad bi čitav svoj duh k sebi vratio,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
sva bića bi odjednom izdahnula i u prah bi se pretvorio čovjek.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Ako razuma imaš, slušaj ovo, prikloni uho glasu riječi mojih.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Može li vladat' koji mrzi pravo? Najpravednijeg hoćeš li osudit'? -
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Onog koji kaže kralju: 'Nitkove!' a odličniku govori: 'Zlikovče!'
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Koji nije spram knezovima pristran i jednak mu je ubog i mogućnik, jer oni su djelo ruku njegovih?
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Zaglave za tren, usred gluhe noći: komešaju se narodi, prolaze; ni od čije ruke moćni padaju.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Jer, on nadzire pute čovjekove, pazi nad svakim njegovim korakom.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Nema toga mraka niti crne tmine gdje bi se mogli zlikovci sakriti.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Bog nikome unaprijed ne kaže kada će na sud pred njega stupiti.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Bez saslušanja on satire jake i stavlja druge na njihovo mjesto.
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
TÓa odveć dobro poznaje im djela! Sred noći on ih obara i gazi.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Ćuškom ih bije zbog zloće njihove na mjestu gdje ih svi vidjeti mogu.
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Jer prestadoše za njime hoditi, zanemariše putove njegove
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
goneć uboge da vape do njega i potlačene da k njemu leleču.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Al' miruje li, tko da njega gane? Zastre li lice, tko ga vidjet' može?
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Nad pucima bdi k'o i nad čovjekom da ne zavlada tko narod zavodi.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Kada bezbožnik Bogu svome kaže: 'Zavedoše me, više griješit neću.
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Ne uviđam li, ti me sad pouči, i ako sam kad nepravdu činio, ubuduće ja činiti je neću!'
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Misliš da Bog mora njega kazniti, dok ti zamisli njegove prezireš? Al' kada ti odlučuješ, a ne ja, mudrost nam svoju istresi dÓe sada!
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Svi ljudi umni sa mnom će se složit' i svatko razuman koji čuje mene:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Nepromišljeno Job je govorio, u riječima mu neima mudrosti.
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Stoga, nek' se Job dokraja iskuša, jer odgovara poput zlikovaca;
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
a svom grijehu još pobunu domeće, među nama on plješće dlanovima i hule svoje na Boga gomila.”