< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
以利戶又說:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
你們智慧人要聽我的話; 有知識的人要留心聽我說。
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
因為耳朵試驗話語, 好像上膛嘗食物。
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
我們當選擇何為是, 彼此知道何為善。
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
約伯曾說:我是公義, 上帝奪去我的理;
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
我雖有理,還算為說謊言的; 我雖無過,受的傷還不能醫治。
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
誰像約伯, 喝譏誚如同喝水呢?
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
他與作孽的結伴, 和惡人同行。
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
他說:人以上帝為樂, 總是無益。
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
所以,你們明理的人要聽我的話。 上帝斷不致行惡; 全能者斷不致作孽。
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
他必按人所做的報應人, 使各人照所行的得報。
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
上帝必不作惡; 全能者也不偏離公平。
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
誰派他治理地, 安定全世界呢?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
他若專心為己, 將靈和氣收歸自己,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
凡有血氣的就必一同死亡; 世人必仍歸塵土。
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
你若明理,就當聽我的話, 留心聽我言語的聲音。
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
難道恨惡公平的可以掌權嗎? 那有公義的、有大能的,豈可定他有罪嗎?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
他對君王說:你是鄙陋的; 對貴臣說:你是邪惡的。
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
他待王子不徇情面, 也不看重富足的過於貧窮的, 因為都是他手所造。
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
在轉眼之間,半夜之中, 他們就死亡。 百姓被震動而去世; 有權力的被奪去非借人手。
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
上帝注目觀看人的道路, 看明人的腳步。
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
沒有黑暗、陰翳能給作孽的藏身。
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
上帝審判人,不必使人到他面前再三鑒察。
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
他用難測之法打破有能力的人, 設立別人代替他們。
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
他原知道他們的行為, 使他們在夜間傾倒滅亡。
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
他在眾人眼前擊打他們, 如同擊打惡人一樣。
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
因為他們偏行不跟從他, 也不留心他的道,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
甚至使貧窮人的哀聲達到他那裏; 他也聽了困苦人的哀聲。
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
他使人安靜,誰能擾亂呢? 他掩面,誰能見他呢? 無論待一國或一人都是如此-
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
使不虔敬的人不得作王, 免得有人牢籠百姓。
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
有誰對上帝說: 我受了責罰,不再犯罪;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
我所看不明的,求你指教我; 我若作了孽,必不再作?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
他施行報應, 豈要隨你的心願、叫你推辭不受嗎? 選定的是你,不是我。 你所知道的只管說吧!
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
明理的人和聽我話的智慧人必對我說:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
約伯說話沒有知識, 言語中毫無智慧。
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
願約伯被試驗到底, 因他回答像惡人一樣。
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
他在罪上又加悖逆; 在我們中間拍手, 用許多言語輕慢上帝。

< Ayuba 34 >