< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
厄里烏接著說:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
你們有智慧的人,請聽我言;你們明白人,請側耳聽我。
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
原來耳朵是為辨別言語,有如口腔是為辨嘗食物。
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
讓我們來檢討一下誰為正義,讓我們看看何者為善。
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
約伯說過:「我是無罪的,但我的理,卻為天主奪去。
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
我雖無罪無辜,卻成了說謊者;我雖未行不義,卻受了不可醫治的創傷。」
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
那有一人像約伯,肆口漫罵如飲水﹖
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
他豈不是與作惡的人結夥,同壞人交結來往﹖
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
他豈不是說過:「盡心悅樂天主,為人能有什麼好處﹖」
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
為此,你們心地明白的人,請聽我說,天主決不行惡,全能者決無不義!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
他必照人的行為報答他,按他的品行對待他。
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
天主絕對不能作惡,全能者絕對不能顛倒是非。
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
誰委派他掌管大地,誰任命他治理普世﹖
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
他若將自己的神魂收回,將氣息復歸於自己,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
所有血肉的人必都消滅,世人都要歸於塵土。
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
若你聰明,請聽這事,側耳傾聽我的話。
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
憎恨正義的,豈能掌權﹖而你竟敢定那至公義者的罪﹖
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
他能稱君王為歹徒,能稱官吏為壞人。
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
他對權貴不顧情面,亦不重富輕貧,因為都是他一手造成的。
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
他們猝然在半夜死去,貴族能立即氣絕逝世;他剷除權貴者,無須人手。
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
因為他的眼監視人的動作,觀察他的行徑。
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
沒有黑暗,也沒有陰影,可將作惡的人掩蔽。
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
天主不必給人指定時間,為使人到他前去受審。
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
他粉碎權勢者,無須審察,即刻能派定別人代替他們。
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
他原知道他們的行為,一夜之間將他們推翻消滅。
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
在眾目昭彰之下,鞭打他們有如罪犯。
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
因為他們遠離了他,不重視他一切的道,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
致使窮人的哀號上達於他,使他聽到了受苦者的哀求。
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
他若安息,誰敢騷擾﹖他若掩面,誰敢窺視﹖他對國對人都予以監視,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
使凡欺壓人民的,不得為王。
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
如果惡人向天主說:「我受了欺騙,以後不再作惡。
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
我所看不透的,求你指教我;我若以前作了孽,不敢再做了。」
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
他施行報應,豈應隨你的心意﹖或者你能拒絕不受嗎﹖決定的是你,而不是我! 你若知道,儘管說罷!
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
但是心地聰明,具有智慧,且聽我說話的人,必要對我說:「
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
約伯所講的話毫無知識,他的話全不明智。」
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
為此,約伯還要受徹底的究察,因為他的答覆好似出自惡人之口,
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
因為他在罪上又加反叛,當著我們磨拳擦掌,講出許多相反天主的話。

< Ayuba 34 >