< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Sin embargo, Job, escucha ahora mis razones y atiende todas mis palabras.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Ciertamente ahora abro mi boca. Mi lengua habla en mi paladar.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Mis palabras declararán la rectitud de mi corazón y lo que saben mis labios lo dicen con sinceridad:
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
El Espíritu de ʼElohim me hizo y el soplo de ʼEL-Shadday me dio vida.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Respóndeme si puedes. Alístate y ponte en pie ante mí.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Ciertamente pertenezco a ʼEL, como tú. Del barro también fui formado.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Ciertamente mi terror no te espantará, ni mi mano será demasiado pesada sobre ti.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
En verdad tú dijiste a oídos míos. Yo oí el sonido de tus palabras:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
Limpio soy, sin transgresión. Soy inocente y no hay culpa en mí.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Ciertamente Él inventa pretextos contra mí y me considera su enemigo.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Puso mis pies en el cepo y vigila todos mis pasos.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Ciertamente yo te respondo: En esto no eres justo, porque ʼElohim es mayor que el hombre.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
¿Por qué contiendes con ʼEL? Pues Él no da cuenta de ninguna de sus obras.
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Porque ʼElohim habla de una manera o de otra, pero nadie lo percibe:
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
En sueño, en visión nocturna, cuando el sopor cae sobre los hombres, mientras se adormecen en la cama,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Él abre el oído de los hombres y sella su instrucción para ellos,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
a fin de apartar al hombre de su obra y destruir la soberbia del varón,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
para librar su alma del sepulcro y que su vida no perezca a filo de espada.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
También sobre su cama es reprendido con dolores, con el dolor incesante de sus huesos,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
lo cual hace que le repugne el pan, y aun el manjar más delicado.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Su carne se consume hasta que no se ve, y sus huesos, que no se veían, aparecen.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Su alma se acerca al sepulcro y su vida a los que causan la muerte.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Si hay un ángel que sea mediador para él, muy escogido entre 1.000, que recuerda al hombre lo correcto para él,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
tenga compasión de él y diga: Líbrenlo de bajar al sepulcro, pues le hallé un rescate.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Entonces su carne sería más tierna que la de un joven que vuelve al vigor de los días de su juventud.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Invocaría a ʼEloha. Él le haría sacrificio que apacigua, para que vea el semblante de ʼEL con gozo y Él le restaure su justicia al hombre.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Él mira a los hombres y al que dice: Pequé y pervertí lo recto, pero nada me aprovechó,
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Él le redimirá su alma para que no baje al sepulcro, y su vida verá la luz.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
En verdad ʼEL hace todas estas cosas con el hombre dos veces, y aun tres,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
para rescatar su alma del sepulcro e iluminarlo con la luz de la vida.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Presta atención, Job, escúchame. Calla, y permíteme hablar.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Si tienes palabras, respóndeme. Habla, porque yo quiero declararte justo.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Si no, escúchame. Calla, y yo te enseñaré sabiduría.

< Ayuba 33 >