< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
“Ahora escúchame, Job. Presta atención a todo lo que tengo que decir.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Mira, estoy a punto de hablar; mi boca está lista para hablar.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Mis palabras salen de mi corazón recto; mis labios hablan con sinceridad de lo que sé.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
El espíritu de Dios me hizo, y el aliento del Todopoderoso me da vida.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Contéstame, si puedes. Ponte delante de mí y prepárate para defenderte:
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Ante Dios los dos somos iguales. Yo también fui hecho de un pedazo de arcilla.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
No tienes que tener miedo de mí, pues no seré demasiado duro contigo.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Has hablado en mi oído y he escuchado todo lo que tenías que decir.
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
Dices: ‘Estoy limpio, no he hecho nada malo; soy puro, no he pecado.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Mira cómo Dios encuentra faltas en mí y me trata como su enemigo.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Pone mis pies en el cepo y vigila todo lo que hago’.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Pero te equivocas. Déjame explicarte: Dios es más grande que cualquier ser humano.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
¿Por qué luchas contra él, quejándote de que Dios no responde a tus preguntas?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Dios habla una y otra vez, pero la gente no se da cuenta.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
A través de sueños y visiones en la noche, cuando la gente cae en el sueño profundo, descansando en sus camas,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Dios les habla con advertencias solemnes
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
para alejarlos de hacer el mal y evitar que se vuelvan orgullosos.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Los salva de la tumba y los libra de la muerte violenta.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
La gente también es disciplinada en un lecho de dolor, con un dolor constante en sus huesos.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
No tienen deseos de comer; ni siquiera quieren sus platos favoritos.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Su carne se desgasta hasta quedar en nada; todo lo que queda es piel y huesos.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Están a punto de morir; su vida se acerca al verdugo.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
“Pero si aparece un ángel, un mediador, uno de los miles de ángeles de Dios, para indicarle a alguien el camino correcto para ellos,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
tendrá gracia con ellos. Les dirá: ‘Sálvenlos de bajar a la tumba, porque he encontrado un camino para liberarlos’.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Entonces sus cuerpos se renovarán como si fueran jóvenes de nuevo; serán tan fuertes como cuando estaban en la flor de la vida.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Orarán a Dios, y él los aceptará; llegarán a la presencia de Dios con alegría, y él les arreglará las cosas.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Cantarán y dirán a los demás: ‘He pecado, he desvirtuado lo que es justo, pero no me ha servido de nada.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Me salvó de bajar al sepulcro y viviré en la luz’.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Mira, Dios hace esto una y otra vez para la gente;
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
los salva de la tumba para que vean la luz de la vida.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
“Presta atención, Job, y escúchame. Calla y déjame hablar.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Pero si tienes algo que decir, habla.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Si no, escúchame. Calla y te enseñaré la sabiduría”.

< Ayuba 33 >