< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Чуј дакле, Јове, беседу моју, и слушај све речи моје.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Ево, сад отварам уста своја; говори језик мој у устима мојим.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
По правом срцу мом биће речи моје, и мисао чисту изрећи ће усне моје.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Дух Божји створио ме је, и дах Свемогућега дао ми је живот.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Ако можеш, одговори ми, приправи се и стани ми на супрот.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Ево, ја ћу бити место Бога, као што си рекао; од кала сам начињен и ја.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Ето, страх мој неће те страшити, и рука моја неће те тиштати.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Рекао си, дакле, преда мном, и чуо сам глас твојих речи:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
Чист сам, без греха, прав сам и нема безакоња на мени.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Ево, тражи задевицу са мном, држи ме за свог непријатеља.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Меће у кладе ноге моје, вреба по свим стазама мојим.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Ето, у том ниси праведан, одговарам ти; јер је Бог већи од човека.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Зашто се преш с Њим, што за сва дела своја не одговара?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Један пут говори Бог и два пута; али човек не пази.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
У сну, у утвари ноћној, кад тврд сан падне на људе, кад спавају у постељи,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Тада отвара ухо људима и науку им запечаћава,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
Да би одвратио човека од дела његовог, и заклонио од њега охолост;
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Да би сачувао душу његову од јаме, и живот његов да не наиђе на мач.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
И кара га боловима на постељи његовој, и све кости његове тешком болешћу.
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
Тако да се животу његовом гади хлеб и души његовој јело најмилије;
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Нестаје тела његовог на очиглед, и измалају се кости његове, које се пре нису виделе,
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
И душа се његова приближава гробу, и живот његов смрти.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Ако има гласника, тумача, једног од хиљаде, који би казао човеку дужност његову,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Тада ће се смиловати на њ, и рећи ће: Избави га да не отиде у гроб; нашао сам откуп.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
И подмладиће се тело његово као у детета, и повратиће се на дане младости своје,
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Молиће се Богу, и помиловаће га, и гледаће лице његово радујући се, и вратиће човеку по правди његовој.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Гледајући људи рећи ће: Бејах згрешио, и шта је право изврнуо, али ми не поможе.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Он избави душу моју да не отиде у јаму, и живот мој да гледа светлост.
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Гле, све ово чини Бог два пута и три пута човеку,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
Да би повратио душу његову од јаме, да би га обасјавала светлост живих.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Пази, Јове, слушај ме, ћути, да ја говорим.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Ако имаш шта рећи, одговори ми; говори, јер сам те рад оправдати;
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Ако ли не, слушај ти мене; ћути, и научићу те мудрости.