< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Portanto, Jó, ouve, por favor, meus dizeres, e dá ouvidos a todas as minhas palavras.
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Eis que já abri minha boca; minha língua já fala debaixo do meu céu da boca.
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Meus dizeres pronunciarão a integridade do meu coração, e o puro conhecimento dos meus lábios.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
O Espírito de Deus me fez, e o sopro do Todo-Poderoso me deu vida.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Se puderes, responde-me; dispõe-te perante mim, e persiste.
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Eis que para Deus eu sou como tu; do barro também eu fui formado.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Eis que meu terror não te espantará, nem minha mão será pesada sobre ti.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Certamente tu disseste a meus ouvidos, e eu ouvi a voz de tuas palavras,
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
[Que diziam]: Eu sou limpo e sem transgressão; sou inocente, e não tenho culpa.
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Eis que [Deus] buscou pretextos contra mim, [e] me tem por seu inimigo.
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
Ele pôs meus pés no tronco, e observa todas as minhas veredas.
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Eis que nisto não foste justo, eu te respondo; pois Deus é maior que o ser humano.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Por que razão brigas contra ele por não dar resposta às palavras do ser humano?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Contudo Deus fala uma ou duas vezes, ainda que [o ser humano] não entenda.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Em sonho [ou em] visão noturna, quando o sono profundo cai sobre as pessoas, [e] adormecem na cama.
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
Então o revela ao ouvido das pessoas, e os sela com advertências;
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
Para desviar ao ser humano de sua obra, e do homem a soberba.
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Para desviar a sua alma da perdição, e sua vida de passar pela espada.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Também em sua cama é castigado com dores, com luta constante em seus ossos,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
De modo que sua vida detesta [até] o pão, e sua alma a comida deliciosa.
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
Sua carne desaparece da vista, e seus ossos, que antes não se viam, aparecem.
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
Sua alma se aproxima da cova, e sua vida dos que causam a morte.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Se com ele, pois, houver algum anjo, algum intérprete; um dentre mil, para anunciar ao ser humano o que lhe é correto,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
Então [Deus] terá misericórdia dele, e [lhe] dirá: Livra-o, para que não desça à perdição; [já] achei o resgate.
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Sua carne se rejuvenescerá mais do que era na infância, [e] voltará aos dias de sua juventude.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Ele orará a Deus, que se agradará dele; e verá sua face com júbilo, porque ele restituirá ao ser humano sua justiça.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Ele olhará para as pessoas, e dirá: Pequei, e perverti o [que era] correto, o que de nada me aproveitou.
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
[Porém] Deus livrou minha alma para que eu não passasse à cova, e [agora] minha vida vê a luz!
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Eis que Deus faz tudo isto duas [ou] três vezes com o ser humano,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
Para desviar sua alma da perdição, e o iluminar com a luz dos viventes.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Presta atenção, Jó, e ouve-me; cala-te, e eu falarei.
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Se tiveres o que dizer, responde-me; fala, porque eu quero te justificar.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
E se não, escuta-me; cala-te, e eu ensinarei sabedoria.