< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
audi igitur Iob eloquia mea et omnes sermones meos ausculta
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
ecce aperui os meum loquatur lingua mea in faucibus meis
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
simplici corde meo sermones mei et sententiam labia mea puram loquentur
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
spiritus Dei fecit me et spiraculum Omnipotentis vivificavit me
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
si potes responde mihi et adversus faciem meam consiste
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
ecce et me sicut et te fecit Deus et de eodem luto ego quoque formatus sum
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
verumtamen miraculum meum non te terreat et eloquentia mea non sit tibi gravis
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
dixisti ergo in auribus meis et vocem verborum audivi
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
mundus sum ego absque delicto inmaculatus et non est iniquitas in me
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
quia querellas in me repperit ideo arbitratus est me inimicum sibi
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
posuit in nervo pedes meos custodivit omnes semitas meas
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
hoc est ergo in quo non es iustificatus respondebo tibi quia maior sit Deus homine
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
adversum eum contendis quod non ad omnia verba responderit tibi
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
semel loquitur Deus et secundo id ipsum non repetit
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
per somnium in visione nocturna quando inruit sopor super homines et dormiunt in lectulo
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
tunc aperit aures virorum et erudiens eos instruit disciplinam
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
ut avertat hominem ab his quae facit et liberet eum de superbia
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
eruens animam eius a corruptione et vitam illius ut non transeat in gladium
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
increpat quoque per dolorem in lectulo et omnia ossa eius marcescere facit
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
abominabilis ei fit in vita sua panis et animae illius cibus ante desiderabilis
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
tabescet caro eius et ossa quae tecta fuerant nudabuntur
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
adpropinquabit corruptioni anima eius et vita illius mortiferis
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
si fuerit pro eo angelus loquens unum de milibus ut adnuntiet hominis aequitatem
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
miserebitur eius et dicet libera eum et non descendat in corruptionem inveni in quo ei propitier
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
consumpta est caro eius a suppliciis revertatur ad dies adulescentiae suae
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
deprecabitur Deum et placabilis ei erit et videbit faciem eius in iubilo et reddet homini iustitiam suam
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
respiciet homines et dicet peccavi et vere deliqui et ut eram dignus non recepi
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
liberavit animam suam ne pergeret in interitum sed vivens lucem videret
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
ecce haec omnia operatur Deus tribus vicibus per singulos
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
ut revocet animas eorum a corruptione et inluminet luce viventium
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
adtende Iob et audi me et tace dum ego loquar
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
si autem habes quod loquaris responde mihi loquere volo enim te apparere iustum
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
quod si non habes audi me tace et docebo te sapientiam