< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
그런즉 욥이여 내 말을 들으며 나의 모든 말에 귀를 기울이기를 원하노라
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
내가 입을 여니 내 혀가 입에서 동하는구나
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
내 말이 내 마음의 정직함을 나타내고 내 입술이 아는 바를 진실히 말하리라
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
하나님의 신이 나를 지으셨고 전능자의 기운이 나를 살리시느니라
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
네가 할 수 있거든 일어서서 내게 대답하고 내 앞에 진술하라
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
나와 네가 하나님 앞에서 일반이니 나도 흙으로 지으심을 입었은즉
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
내 위엄으로는 너를 두렵게 하지 못하고 내 권세로는 너를 누르지 못하느니라
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
네가 실로 나의 듣는데 말하였고 나는 네 말소리를 들었느니라 이르기를
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
나는 깨끗하여 죄가 없고 허물이 없으며 불의도 없거늘
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
하나님이 나를 칠 틈을 찾으시며 나를 대적으로 여기사
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
내 발을 착고에 채우시고 나의 모든 길을 감시하신다 하였느니라
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
내가 네게 대답하리라 이 말에 네가 의롭지 못하니 하나님은 사람보다 크심이니라
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
하나님은 모든 행하시는 것을 스스로 진술치 아니하시나니 네가 하나님과 변쟁함은 어찜이뇨
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
사람은 무관히 여겨도 하나님은 한번 말씀하시고 다시 말씀하시되
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
사람이 침상에서 졸며 깊이 잠들 때에나 꿈에나 밤의 이상 중에
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
사람의 귀를 여시고 인치듯 교훈하시나니
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
이는 사람으로 그 꾀를 버리게 하려 하심이며 사람에게 교만을 막으려 하심이라
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
그는 사람의 혼으로 구덩이에 빠지지 않게 하시며 그 생명으로 칼에 멸망치 않게 하시느니라
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
혹시는 사람이 병상의 고통과 뼈가 늘 쑤심의 징계를 받나니
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
그의 마음은 식물을 싫어하고 그의 혼은 별미를 싫어하며
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
그의 살은 파리하여 보이지 아니하고 보이지 않던 뼈가 드러나서
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
그의 혼이 구덩이에, 그의 생명이 멸하는 자에게 가까와지느니라
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
그럴 때에 만일 일천 천사 가운데 하나가 그 사람의 해석자로 함께 있어서 그 정당히 행할 것을 보일진대
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
하나님이 그 사람을 긍휼히 여기사 이르시기를 그를 건져서 구덩이에 내려가지 않게 하라 내가 대속물을 얻었다 하시리라
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
그런즉 그 살이 어린 아이보다 연하여져서 소년 때를 회복할 것이요
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
그는 하나님께 기도하므로 하나님이 은혜를 베푸사 그로 자기의 얼굴을 즐거이 보게 하시고 사람에게 그 의를 회복시키시느니라
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
그가 사람 앞에서 노래하여 이르기를 내가 전에 범죄하여 시비를 바꾸었으나 내게 무익하였었구나
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
하나님이 내 영혼을 건지사 구덩이에 내려가지 않게 하셨으니 내생명이 빛을 보겠구나 하리라
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
하나님이 사람에게 이 모든 일을 재삼 행하심은
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
그 영혼을 구덩이에서 끌어 돌이키고 생명의 빛으로 그에게 비취려 하심이니라
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
욥이여 귀를 기울여 내게 들으라 잠잠하라 내가 말하리라
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
만일 할 말이 있거든 대답하라 내가 너를 의롭게 하려 하노니 말하라
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
만일 없으면 내 말을 들으라 잠잠하라 내가 지혜로 너를 가르치리라

< Ayuba 33 >