< Ayuba 33 >
1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
Doch höre nun, Hiob, meine Rede, und fasse alle meine Worte!
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Siehe doch, ich öffne meinen Mund, es redet die Zunge an meinem Gaumen;
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
Meine Reden kommen aus aufrichtigem Herzen, und meine Lippen sprechen lautere Wahrheit aus.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Der Geist Gottes hat mich gemacht, und der Odem des Allmächtigen belebt mich.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Kannst du es, so widerlege mich; rüste dich, tritt vor mich hin!
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Siehe, ich stehe zu Gott, gleich wie du; auch ich bin vom Lehm genommen.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Siehe, Furcht vor mir soll dich nicht schrecken, und ich will dir nicht lästig sein.
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
Nun hast du vor meinen Ohren gesagt, und ich habe deine eigenen Worte gehört:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
«Rein bin ich, ohne Vergehen, unbefleckt und ohne Schuld!
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Siehe, er erfindet Beschuldigungen gegen mich, er hält mich für seinen Feind;
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
er legt meine Füße in den Stock und lauert auf alle meine Schritte.»
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Siehe, das sagst du nicht mit Recht, darauf muß ich dir antworten; denn Gott ist größer als der Mensch.
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Warum haderst du denn mit ihm, da er doch keine seiner Taten zu verantworten hat?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Sondern Gott redet einmal und zum zweitenmal, aber man beachtet es nicht.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Im Traum, im Nachtgesicht, wenn tiefer Schlaf die Menschen befällt und sie in ihren Betten schlafen,
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
da öffnet er das Ohr der Menschen und besiegelt seine Warnung an sie,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
damit der Mensch von seinem Tun abstehe und er den Mann vor Übermut beschütze,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
daß er seine Seele von der Grube zurückhalte, und sein Leben, daß er nicht renne ins Geschoß.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Er züchtigt ihn mit Schmerzen auf seinem Lager, ein hartes Gericht geht über seinen Leib,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
daß ihm das Brot zum Ekel wird, seiner Seele die Lieblingsspeise;
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
sein Fleisch schwindet dahin, man sieht es nicht mehr, und seine Gebeine, die man sonst nicht sah, werden bloß;
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
seine Seele naht sich der Grube und sein Leben den Todesmächten.
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
Wenn es dann für ihn einen Engel gibt, einen Mittler, einen aus Tausenden, der dem Menschen verkündigt seine Gerechtigkeit;
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
wenn er sich über ihn erbarmt und spricht: «Erlöse ihn, daß er nicht zur Grube hinabfahre; ich habe ein Lösegeld gefunden!»
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
Alsdann wird sein Fleisch wieder grünen von Jugendfrische, er wird wiederkehren zu den Tagen seiner Jugend;
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
er wird zu Gott bitten, der wird ihm gnädig sein, ihn sein Angesicht mit Jauchzen sehen lassen und dem Menschen seine Gerechtigkeit wiedergeben.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Er wird singen vor den Menschen und sagen: Ich hatte gesündigt und das Recht verkehrt; aber er hat mir nicht vergolten nach Verdienst;
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
er hat meine Seele erlöst, daß sie nicht in die Grube gefahren ist, so daß mein Leben das Licht wieder sieht!
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
Siehe, dies alles tut Gott zwei oder dreimal mit dem Menschen,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
daß er seine Seele vom Verderben herumhole und ihn erleuchte mit dem Lichte der Lebendigen.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Merke auf, Hiob, höre mir zu, schweige, und ich will reden!
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Hast du aber Worte, so antworte mir, sage her, denn ich wünsche deine Rechtfertigung;
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
wo aber nicht, so höre mir zu, schweige, und ich will dich Weisheit lehren!