< Ayuba 33 >

1 “Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
»Nun aber höre, Hiob, meine Reden und leihe dein Ohr allen meinen Worten!
2 Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
Wisse wohl: wenn ich meinen Mund jetzt auftue und meine Zunge sich vernehmlich hören läßt,
3 Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
so sind meine Worte aufrichtig wie mein Herz, und was meine Lippen wissen, sprechen sie unverfälscht aus.
4 Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Der Geist Gottes, der mich geschaffen hat, und der Hauch des Allmächtigen belebt mich.
5 Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
Wenn du’s vermagst, so widerlege mich: rüste dich mit Beweisgründen gegen mich, tritt an zum Kampf!
6 Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Siehe, ich stehe zu Gott ebenso wie du: aus Ton bin auch ich gebildet.
7 Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Nein, Angst vor mir braucht dich nicht einzuschüchtern, und meine Wucht soll dich nicht niederdrücken!«
8 “Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
»Nun aber hast du vor meinen Ohren ausgesprochen, und deutlich habe ich deine Worte gehört:
9 ‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
›Unschuldig bin ich, ohne Missetat, rein bin ich, und kein Vergehen haftet mir an!
10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
Fürwahr, er (Gott) erfindet Feindseligkeiten gegen mich, sieht in mir einen Feind;
11 ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
er legt meine Füße in den Block, überwacht alle meine Pfade.‹
12 “Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Sieh, darin hast du unrecht, entgegne ich dir; denn Gott ist größer als ein Mensch.«
13 Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
»Warum hast du den Vorwurf gegen ihn erhoben, daß er dir auf alle deine Worte keine Antwort gebe?
14 Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
Vielmehr redet Gott einmal und zweimal, man achtet nur nicht darauf.
15 A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
Im Traum, im Nachtgesicht, wenn tiefer Schlaf die Menschen befällt, im Schlummerzustand auf dem Lager:
16 mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
da öffnet er den Menschen das Ohr und schreckt sie durch Verwarnung,
17 don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
um den Menschen von seinem (bösen) Tun abzubringen und den Mann vor Überhebung zu behüten,
18 don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
um seine Seele vor der Grube zu bewahren und sein Leben vor dem Geschoß des Todes.
19 “Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
Auch wird er durch Schmerzen auf seinem Lager in Zucht genommen und durch andauernden Leidenskampf in seinen Gliedern,
20 yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
so daß für seinen Lebenstrieb alle Nahrung zum Ekel wird und für seine Eßlust sogar die Lieblingsspeise;
21 Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
sein Fleisch schwindet dahin, daß es nicht mehr zu sehen ist, und seine vordem verborgenen Knochen treten zu Tage,
22 Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
so daß seine Seele der Grube nahe kommt und sein Leben den Todesmächten.«
23 Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
»Wenn dann ein Engel für ihn da ist, ein Fürsprecher, ein einziger aus den tausend, um für den Menschen Zeugnis von seiner Gerechtigkeit abzulegen,
24 yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
und dieser sich seiner erbarmt und (zu Gott) spricht: ›Laß ihn frei, daß er nicht in die Grube hinabfährt! Ich habe eine Sühne gefunden‹,
25 Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
so strotzt sein Leib wieder von Jugendkraft, so daß er in die Tage seines Jünglingsalters zurückversetzt wird.
26 Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
Er betet zu Gott, und dieser nimmt ihn gnädig an, läßt ihn sein Angesicht unter Jauchzen schauen und gibt dem Menschen seine Gerechtigkeit zurück.
27 Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
Er singt vor dem Volke und bekennt: ›Ich hatte gesündigt und das Recht verkehrt, aber es ist mir nicht vergolten worden!
28 Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
Erlöst hat (Gott) meine Seele, daß sie nicht in die Grube gefahren ist, und mein Leben erfreut sich am Anblick des Lichts!‹«
29 “Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
»Sieh, dies alles tut Gott zweimal, ja dreimal an dem Menschen,
30 Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
um seine Seele von der Grube fernzuhalten und damit er vom Licht des Lebens umleuchtet werde.
31 “Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
Merke auf, Hiob, höre mir zu, schweige und laß mich reden!
32 In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
Hast du etwas einzuwenden, so widerlege mich; sprich, denn ich möchte dich gern rechtfertigen.
33 Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”
Hast du aber nichts, so höre mir zu; schweige, damit ich dich Weisheit lehre!«

< Ayuba 33 >